ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Samu Gawar Mutum 15, Shanu 2000 Sun Bace Da Kone Mana Gidaje 78 A Jihar Filato – MACBAN

by Muhammad
3 years ago
MACBAN

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) a ranar Lahadi ta ce an kashe mutane 15 bayan wani farmaki da ake zargin kai musu a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato.

Kungiyar ta kuma ce an kona gidaje 78 na mambobinta yayin da sama da shanu 2,000 suka bace bayan farmakin.

  • Ana Ci Gaba Da Zaman Gida A Yankin Mangu Ta Jihar Filato Kan Sanya Dokar Hana Fita Na Sa’o’i 24
  • An Kashe Mutum 2, An Raunata 3 A Wani Sabon Hari A Filato

Nuru Abdullahi, shugaban kungiyar na jihar ne ya bayyana hakan ga manema labarai jiya, a Jos, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

Daily Trust ta ruwaito cewa a ranar Asabar din da ta gabata kungiyar ta zargi ‘Operation Rainbow’, jami’an tsaron jihar da kai wa yankinsu hari tare da kunna musu wuta, zargin da rundunar ta musanta.

Ya ce, “A harin da aka kai a kauyukan Mangu, mun gano gawarwaki 15 da aka kashe a ranar Juma’a. Kimanin gidaje 78 ne suka kone. Shanu da adadinsu ya kai 2,000 har yanzu ba a gansu ba. Wannan abin takaicin ne a jihar.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Abdullahi ya kuma yi zargin wani shiri na kai wa al’ummarsu hari da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne.

“Akwai rahoton sirri da ke nuna cewa akwai kwararrun ‘yan bindiga da aka dauka aka kawo su yaki tare da fatattakar duk Fulani daga jihar Filato da sunan rikici. Don haka a halin yanzu muna kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta kawo karshen abin da ke faruwa a karamar hukumar Mangu.

“Ya kamata su dauki matakin gaggawa kafin al’amura su wuce gona da iri. Muna rokon Gwamnatin tarayya da ta dauki matakin da ya dace don kada al’amura su fita daga hannunsu. Ba za mu ci gaba da kallon yadda mutane ke kashe mu da lalata mana dukiyoyi ba,” Abdullahi ya kara da cewa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, da na runduna ta uku ta rundunar sojojin Nijeriya, Rukuba Barrack, Laftanar Kanar Ishaku Sabastine Takwa, har yanzu ba su amsa kira da sakon da wakilin na Trust ya yi musi kan lamarin ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

An samu rikici a kauyukan karamar hukumar Mangu inda aka tabbatar da mutuwar mutane sama da 200 da suka hada da mata da kananan yara a watannin baya.

A halin da ake ciki gwamnan jihar Filato Caleb Mutfwang ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a karamar hukumar Mangu don saisaita al’amura dakile asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.

MACBAN
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
An Kubutar Da Mutum 30 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Birnin Kebbi

An Kubutar Da Mutum 30 Daga Hannun 'Yan Bindiga A Birnin Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.