ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Samu Gawar Mutum 15, Shanu 2000 Sun Bace Da Kone Mana Gidaje 78 A Jihar Filato – MACBAN

by Muhammad
3 years ago
MACBAN

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) a ranar Lahadi ta ce an kashe mutane 15 bayan wani farmaki da ake zargin kai musu a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato.

Kungiyar ta kuma ce an kona gidaje 78 na mambobinta yayin da sama da shanu 2,000 suka bace bayan farmakin.

  • Ana Ci Gaba Da Zaman Gida A Yankin Mangu Ta Jihar Filato Kan Sanya Dokar Hana Fita Na Sa’o’i 24
  • An Kashe Mutum 2, An Raunata 3 A Wani Sabon Hari A Filato

Nuru Abdullahi, shugaban kungiyar na jihar ne ya bayyana hakan ga manema labarai jiya, a Jos, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT

Daily Trust ta ruwaito cewa a ranar Asabar din da ta gabata kungiyar ta zargi ‘Operation Rainbow’, jami’an tsaron jihar da kai wa yankinsu hari tare da kunna musu wuta, zargin da rundunar ta musanta.

Ya ce, “A harin da aka kai a kauyukan Mangu, mun gano gawarwaki 15 da aka kashe a ranar Juma’a. Kimanin gidaje 78 ne suka kone. Shanu da adadinsu ya kai 2,000 har yanzu ba a gansu ba. Wannan abin takaicin ne a jihar.”

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

Abdullahi ya kuma yi zargin wani shiri na kai wa al’ummarsu hari da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne.

“Akwai rahoton sirri da ke nuna cewa akwai kwararrun ‘yan bindiga da aka dauka aka kawo su yaki tare da fatattakar duk Fulani daga jihar Filato da sunan rikici. Don haka a halin yanzu muna kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta kawo karshen abin da ke faruwa a karamar hukumar Mangu.

“Ya kamata su dauki matakin gaggawa kafin al’amura su wuce gona da iri. Muna rokon Gwamnatin tarayya da ta dauki matakin da ya dace don kada al’amura su fita daga hannunsu. Ba za mu ci gaba da kallon yadda mutane ke kashe mu da lalata mana dukiyoyi ba,” Abdullahi ya kara da cewa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, da na runduna ta uku ta rundunar sojojin Nijeriya, Rukuba Barrack, Laftanar Kanar Ishaku Sabastine Takwa, har yanzu ba su amsa kira da sakon da wakilin na Trust ya yi musi kan lamarin ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

An samu rikici a kauyukan karamar hukumar Mangu inda aka tabbatar da mutuwar mutane sama da 200 da suka hada da mata da kananan yara a watannin baya.

A halin da ake ciki gwamnan jihar Filato Caleb Mutfwang ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a karamar hukumar Mangu don saisaita al’amura dakile asarar rayuka da dukiyoyi a yankin.

MACBAN
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81
Labarai

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Next Post
An Kubutar Da Mutum 30 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Birnin Kebbi

An Kubutar Da Mutum 30 Daga Hannun 'Yan Bindiga A Birnin Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
MACBAN

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.