• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Siyasa
0
Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar NNPP Injiniya Nura Khalil ya bayyana cewa sun shirya korar jami’yyar APC daga mulki a zaɓe mai zuwa saboda yadda gwamnati ta ƙksa yin abin azo a gani a shekaru takwas da ta kwashe tana shugabanci

Nura Khalil ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake ƙaddamar da gangamin yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi ta jihar Katsina.

Injiniya wanda ya ce yanzu jihar Katsina bata da sauran komi na ƙaddara, bata da gidaje bata da filaye komi ya kare, ya ce bai taɓa ganin mutane masu ɓarna ba kamar wannan gwamnati.

Ya kara da cewa jihar Katsina na neman mutum da yasan hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da za a yi jihar aikin cigaba saboda yadda aka naƙasata a mulkin ‘yan bani na iya.

Haka kuma bayyana cewa dalilin da yasa ya fara wannan yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi shi ne, suna da wani sirri wanda su da Daurawa a jihar Jigawa da kuma Kankia ke da tataccen hasken rana da zai iya samar da haske wuta mai karfin ‘Megawat’ 1,000

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

“Idan na samu nasarar lashe zaɓe zan yi amfani da wannan damar wajan samarwa jihar Katsina kuɗin shiga kimanin biliyan 100 duk shekara kuma cikin shekaru huɗu zuwa biyar za su iya kaiwa biliyan 4 ko fiye da haka ta hanyar hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana” inji shi

A cewar sa idan aka samu nasarar yin aiki hakan zai ba jihar Katsina damar yin gogayya da jihohi irinsu Kano da kuma Legas da fuskar kasuwanci da sauran sha’anin tattalin arziki da noma da kuma tsaro baki ɗaya.

Injiniya Nura Khalil da ya juya akan batun zaɓe ya ja hankalin matasa da su tabbatar sun zaɓi jam’iyyar NNPP domin samun mafita a wannan rayuwa da ta zama ba tabbas a ƙarƙashin mulkin APC

Yana mai kira ga mata waɗanda ake yaudara ana karɓar katin zaɓen su, da sunan za a ba su Naira dubu 10 zuwa ashirin, wanda ya ce daga ƙarshe ɗari biyar ake ba su.

“mata kuma da rawar da zaku taka wajan ganin jami’yyar NNPP ta samu nasarar lashe zaɓe daga sama har ƙasa ta hanyar tabbatar da cewa an zaɓi jam’iyyar mai alama kayan marmari.

Daga ƙarshe ya yi kira da a zaɓi injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso a matsayin shugaban ƙasa sannan a zaɓi sauran’yan takarar jam’iyyar NNPP a dukkanin matakai domin warware matsalar tsaro da ta addabi yankin arewa da Najeriya baki ɗaya.

Shi ma nasa jawabin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya samu wakilcin ɗan takarar gwamna na jihar Kano Abba Gida Gida ya ce zaɓen jami’yyar NNPP a dukkan matakai shi zai yi maganin matsalolin da ake fama da su.

  • 2023: ‘Yan Damfara Sun Bude Manhajar Intanet Don Daukar Ma’aikatan Zabe – INEC

Abba ya nuna jin daɗin sa da irin tarɓa da karancin da aka nuna masu musamman magoya bayan jami’yyar NNPP na jihar Katsina da suka farin ɗango domin halartar wannan gangami a garin Mashi na jihar Katsina.

Ya yi addu’a da fatan cewa jama’a za su fito kwanso da kwarkwata ranar zaɓe domin kawar da jam’iyyar APC da suka addabi al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Shugaban Kasa Zai Gaji Kasafin Kudin Buhari Na Karshe?

Next Post

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

1 day ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

2 days ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

2 days ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

4 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

5 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

5 days ago
Next Post
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.