ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
APC

Ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar NNPP Injiniya Nura Khalil ya bayyana cewa sun shirya korar jami’yyar APC daga mulki a zaɓe mai zuwa saboda yadda gwamnati ta ƙksa yin abin azo a gani a shekaru takwas da ta kwashe tana shugabanci

Nura Khalil ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake ƙaddamar da gangamin yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi ta jihar Katsina.

Injiniya wanda ya ce yanzu jihar Katsina bata da sauran komi na ƙaddara, bata da gidaje bata da filaye komi ya kare, ya ce bai taɓa ganin mutane masu ɓarna ba kamar wannan gwamnati.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa jihar Katsina na neman mutum da yasan hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da za a yi jihar aikin cigaba saboda yadda aka naƙasata a mulkin ‘yan bani na iya.

Haka kuma bayyana cewa dalilin da yasa ya fara wannan yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi shi ne, suna da wani sirri wanda su da Daurawa a jihar Jigawa da kuma Kankia ke da tataccen hasken rana da zai iya samar da haske wuta mai karfin ‘Megawat’ 1,000

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

“Idan na samu nasarar lashe zaɓe zan yi amfani da wannan damar wajan samarwa jihar Katsina kuɗin shiga kimanin biliyan 100 duk shekara kuma cikin shekaru huɗu zuwa biyar za su iya kaiwa biliyan 4 ko fiye da haka ta hanyar hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana” inji shi

A cewar sa idan aka samu nasarar yin aiki hakan zai ba jihar Katsina damar yin gogayya da jihohi irinsu Kano da kuma Legas da fuskar kasuwanci da sauran sha’anin tattalin arziki da noma da kuma tsaro baki ɗaya.

Injiniya Nura Khalil da ya juya akan batun zaɓe ya ja hankalin matasa da su tabbatar sun zaɓi jam’iyyar NNPP domin samun mafita a wannan rayuwa da ta zama ba tabbas a ƙarƙashin mulkin APC

Yana mai kira ga mata waɗanda ake yaudara ana karɓar katin zaɓen su, da sunan za a ba su Naira dubu 10 zuwa ashirin, wanda ya ce daga ƙarshe ɗari biyar ake ba su.

“mata kuma da rawar da zaku taka wajan ganin jami’yyar NNPP ta samu nasarar lashe zaɓe daga sama har ƙasa ta hanyar tabbatar da cewa an zaɓi jam’iyyar mai alama kayan marmari.

Daga ƙarshe ya yi kira da a zaɓi injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso a matsayin shugaban ƙasa sannan a zaɓi sauran’yan takarar jam’iyyar NNPP a dukkanin matakai domin warware matsalar tsaro da ta addabi yankin arewa da Najeriya baki ɗaya.

Shi ma nasa jawabin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya samu wakilcin ɗan takarar gwamna na jihar Kano Abba Gida Gida ya ce zaɓen jami’yyar NNPP a dukkan matakai shi zai yi maganin matsalolin da ake fama da su.

  • 2023: ‘Yan Damfara Sun Bude Manhajar Intanet Don Daukar Ma’aikatan Zabe – INEC

Abba ya nuna jin daɗin sa da irin tarɓa da karancin da aka nuna masu musamman magoya bayan jami’yyar NNPP na jihar Katsina da suka farin ɗango domin halartar wannan gangami a garin Mashi na jihar Katsina.

Ya yi addu’a da fatan cewa jama’a za su fito kwanso da kwarkwata ranar zaɓe domin kawar da jam’iyyar APC da suka addabi al’umma.

APC
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.