ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
APC

Ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar NNPP Injiniya Nura Khalil ya bayyana cewa sun shirya korar jami’yyar APC daga mulki a zaɓe mai zuwa saboda yadda gwamnati ta ƙksa yin abin azo a gani a shekaru takwas da ta kwashe tana shugabanci

Nura Khalil ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake ƙaddamar da gangamin yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi ta jihar Katsina.

Injiniya wanda ya ce yanzu jihar Katsina bata da sauran komi na ƙaddara, bata da gidaje bata da filaye komi ya kare, ya ce bai taɓa ganin mutane masu ɓarna ba kamar wannan gwamnati.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa jihar Katsina na neman mutum da yasan hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da za a yi jihar aikin cigaba saboda yadda aka naƙasata a mulkin ‘yan bani na iya.

Haka kuma bayyana cewa dalilin da yasa ya fara wannan yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi shi ne, suna da wani sirri wanda su da Daurawa a jihar Jigawa da kuma Kankia ke da tataccen hasken rana da zai iya samar da haske wuta mai karfin ‘Megawat’ 1,000

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

“Idan na samu nasarar lashe zaɓe zan yi amfani da wannan damar wajan samarwa jihar Katsina kuɗin shiga kimanin biliyan 100 duk shekara kuma cikin shekaru huɗu zuwa biyar za su iya kaiwa biliyan 4 ko fiye da haka ta hanyar hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana” inji shi

A cewar sa idan aka samu nasarar yin aiki hakan zai ba jihar Katsina damar yin gogayya da jihohi irinsu Kano da kuma Legas da fuskar kasuwanci da sauran sha’anin tattalin arziki da noma da kuma tsaro baki ɗaya.

Injiniya Nura Khalil da ya juya akan batun zaɓe ya ja hankalin matasa da su tabbatar sun zaɓi jam’iyyar NNPP domin samun mafita a wannan rayuwa da ta zama ba tabbas a ƙarƙashin mulkin APC

Yana mai kira ga mata waɗanda ake yaudara ana karɓar katin zaɓen su, da sunan za a ba su Naira dubu 10 zuwa ashirin, wanda ya ce daga ƙarshe ɗari biyar ake ba su.

“mata kuma da rawar da zaku taka wajan ganin jami’yyar NNPP ta samu nasarar lashe zaɓe daga sama har ƙasa ta hanyar tabbatar da cewa an zaɓi jam’iyyar mai alama kayan marmari.

Daga ƙarshe ya yi kira da a zaɓi injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso a matsayin shugaban ƙasa sannan a zaɓi sauran’yan takarar jam’iyyar NNPP a dukkanin matakai domin warware matsalar tsaro da ta addabi yankin arewa da Najeriya baki ɗaya.

Shi ma nasa jawabin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya samu wakilcin ɗan takarar gwamna na jihar Kano Abba Gida Gida ya ce zaɓen jami’yyar NNPP a dukkan matakai shi zai yi maganin matsalolin da ake fama da su.

  • 2023: ‘Yan Damfara Sun Bude Manhajar Intanet Don Daukar Ma’aikatan Zabe – INEC

Abba ya nuna jin daɗin sa da irin tarɓa da karancin da aka nuna masu musamman magoya bayan jami’yyar NNPP na jihar Katsina da suka farin ɗango domin halartar wannan gangami a garin Mashi na jihar Katsina.

Ya yi addu’a da fatan cewa jama’a za su fito kwanso da kwarkwata ranar zaɓe domin kawar da jam’iyyar APC da suka addabi al’umma.

APC
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.