ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
APC

Ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar NNPP Injiniya Nura Khalil ya bayyana cewa sun shirya korar jami’yyar APC daga mulki a zaɓe mai zuwa saboda yadda gwamnati ta ƙksa yin abin azo a gani a shekaru takwas da ta kwashe tana shugabanci

Nura Khalil ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake ƙaddamar da gangamin yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi ta jihar Katsina.

Injiniya wanda ya ce yanzu jihar Katsina bata da sauran komi na ƙaddara, bata da gidaje bata da filaye komi ya kare, ya ce bai taɓa ganin mutane masu ɓarna ba kamar wannan gwamnati.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa jihar Katsina na neman mutum da yasan hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da za a yi jihar aikin cigaba saboda yadda aka naƙasata a mulkin ‘yan bani na iya.

Haka kuma bayyana cewa dalilin da yasa ya fara wannan yakin neman zaɓen sa a ƙaramar hukumar Mashi shi ne, suna da wani sirri wanda su da Daurawa a jihar Jigawa da kuma Kankia ke da tataccen hasken rana da zai iya samar da haske wuta mai karfin ‘Megawat’ 1,000

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

“Idan na samu nasarar lashe zaɓe zan yi amfani da wannan damar wajan samarwa jihar Katsina kuɗin shiga kimanin biliyan 100 duk shekara kuma cikin shekaru huɗu zuwa biyar za su iya kaiwa biliyan 4 ko fiye da haka ta hanyar hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana” inji shi

A cewar sa idan aka samu nasarar yin aiki hakan zai ba jihar Katsina damar yin gogayya da jihohi irinsu Kano da kuma Legas da fuskar kasuwanci da sauran sha’anin tattalin arziki da noma da kuma tsaro baki ɗaya.

Injiniya Nura Khalil da ya juya akan batun zaɓe ya ja hankalin matasa da su tabbatar sun zaɓi jam’iyyar NNPP domin samun mafita a wannan rayuwa da ta zama ba tabbas a ƙarƙashin mulkin APC

Yana mai kira ga mata waɗanda ake yaudara ana karɓar katin zaɓen su, da sunan za a ba su Naira dubu 10 zuwa ashirin, wanda ya ce daga ƙarshe ɗari biyar ake ba su.

“mata kuma da rawar da zaku taka wajan ganin jami’yyar NNPP ta samu nasarar lashe zaɓe daga sama har ƙasa ta hanyar tabbatar da cewa an zaɓi jam’iyyar mai alama kayan marmari.

Daga ƙarshe ya yi kira da a zaɓi injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso a matsayin shugaban ƙasa sannan a zaɓi sauran’yan takarar jam’iyyar NNPP a dukkanin matakai domin warware matsalar tsaro da ta addabi yankin arewa da Najeriya baki ɗaya.

Shi ma nasa jawabin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya samu wakilcin ɗan takarar gwamna na jihar Kano Abba Gida Gida ya ce zaɓen jami’yyar NNPP a dukkan matakai shi zai yi maganin matsalolin da ake fama da su.

  • 2023: ‘Yan Damfara Sun Bude Manhajar Intanet Don Daukar Ma’aikatan Zabe – INEC

Abba ya nuna jin daɗin sa da irin tarɓa da karancin da aka nuna masu musamman magoya bayan jami’yyar NNPP na jihar Katsina da suka farin ɗango domin halartar wannan gangami a garin Mashi na jihar Katsina.

Ya yi addu’a da fatan cewa jama’a za su fito kwanso da kwarkwata ranar zaɓe domin kawar da jam’iyyar APC da suka addabi al’umma.

APC
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
APC
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.