• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Alfahari Da Dangote  – Tinubu

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Muna Alfahari Da Dangote  – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na alfahari da Dangote kan yadda yake inganta tattalin arzikin kasar nan.

A jiya ne kamfanin Dangote ya samu gagarumar lambar yabo daga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda ya bayyana matsayin gwamnati kan ci gaban da kamfanin ya samu a Nijeriya da ma nahiyar Afirka baki daya.

  • Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya
  • Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

Amincewa da shugabancin ya zo ne bayan karramawa da lambobin yabo da kamfanin ya samu don samar da dubban ayyukan yi da kuma mai tasiri ga tattalin arzikin Nijeriya.

Shugaba Tinubu wanda ya halarci taron tattalin arzikin Nijeriya karo na 29 da ke gudana a Abuja, ya ce: “Kuna da tasiri. Ku ci gaba da yin kyawawan abubuwan da kuke yi. Ku ci gaba da saka hannun jari a Nijeriya.”

Dangote shi ne babban mai daukar ma’aikata bayan gwamnati, kuma daya daga cikin manyan masu hannu da shuni a nahiyar.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

A jawabin da ya gabatar tun farko lokacin da yake bude taron shekara-shekarar, shugaban ya yi kira ga kamfanoni masu zaman kansu da su shiga sahun masu dawo da ci gaban tattalin arzikin Nijeriya, inda ya kara da cewa kasar za ta iya bunkasa ne ta hanyar hadin gwiwa.

Masana da suka yi jawabi a wajen taron sun bayyana cewa Nijeriya na jiran matatar man fetur ta Dangote, inda suka bayyana kwarin gwiwar cewa hakan zai kawo wani gagarumin ci gaba ga tattalin arzikin kasar nan.

Da yake jawabi a wajen taron mai taken: ‘Bude Hanyar Yaki Da Cin Hanci da Rashawa’, Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin Dangote Industries Limited, Mista Olakunle Alake, ya ce ya yi farin ciki da yadda gwamnatin Shugaba Tinubu ta fahimci rawar da kamfanoni ke takawa, tare da karfafa bukatar hadin gwiwa.

Mista Alake ya ce dole ne Nijeriya ta bunkasa tattalin arzikinta musamman bangaren masana’antu domin samun damar taka muhimmiyar rawa a yankin Afirka da bangaren ciniki (AFCFTA).

Ya ce duk da cewa AFCFTA ba ita ce mafita ga tattalin arzikin Nijeriya ba, amma ya yi watsi da cewa kasar nan za ta iya samun tagomashi daga gare ta ta hanyar tallafawa ci gaban masana’antu.

Mista Alake ya bukaci gwamnatocin kasashen Afirka ta Yamma da su gyara matsalolin da ke kawo cikas ga aiwatar da ka’idojin kungiyar ECOWAS, inda ya bayyana cewa har yanzu harkokin kasuwanci a kasashen yammacin Afirka na samun koma baya.

Ya bayar da shawarar inganta iyakokin, tashoshin jiragen ruwa a nahiyar domin samun bunkasar tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaDangoteTaroTattalin ArzikiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Yi Walimar Saukar Alkur’ani Ta ‘Yar Abba El-Mustapha

Next Post

Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

Related

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

15 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 day ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 days ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Next Post
Dawowar Ta’addanci Ta Sake Jefa Sakkwatawa Da Zamfarawa Cikin Zullumi

Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.