• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Alfahari Da Dangote  – Tinubu

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Muna Alfahari Da Dangote  – Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na alfahari da Dangote kan yadda yake inganta tattalin arzikin kasar nan.

A jiya ne kamfanin Dangote ya samu gagarumar lambar yabo daga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda ya bayyana matsayin gwamnati kan ci gaban da kamfanin ya samu a Nijeriya da ma nahiyar Afirka baki daya.

  • Jikar Dantata Ta Rasu Tana Da Shekaru 40 A Duniya
  • Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID

Amincewa da shugabancin ya zo ne bayan karramawa da lambobin yabo da kamfanin ya samu don samar da dubban ayyukan yi da kuma mai tasiri ga tattalin arzikin Nijeriya.

Shugaba Tinubu wanda ya halarci taron tattalin arzikin Nijeriya karo na 29 da ke gudana a Abuja, ya ce: “Kuna da tasiri. Ku ci gaba da yin kyawawan abubuwan da kuke yi. Ku ci gaba da saka hannun jari a Nijeriya.”

Dangote shi ne babban mai daukar ma’aikata bayan gwamnati, kuma daya daga cikin manyan masu hannu da shuni a nahiyar.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

A jawabin da ya gabatar tun farko lokacin da yake bude taron shekara-shekarar, shugaban ya yi kira ga kamfanoni masu zaman kansu da su shiga sahun masu dawo da ci gaban tattalin arzikin Nijeriya, inda ya kara da cewa kasar za ta iya bunkasa ne ta hanyar hadin gwiwa.

Masana da suka yi jawabi a wajen taron sun bayyana cewa Nijeriya na jiran matatar man fetur ta Dangote, inda suka bayyana kwarin gwiwar cewa hakan zai kawo wani gagarumin ci gaba ga tattalin arzikin kasar nan.

Da yake jawabi a wajen taron mai taken: ‘Bude Hanyar Yaki Da Cin Hanci da Rashawa’, Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin Dangote Industries Limited, Mista Olakunle Alake, ya ce ya yi farin ciki da yadda gwamnatin Shugaba Tinubu ta fahimci rawar da kamfanoni ke takawa, tare da karfafa bukatar hadin gwiwa.

Mista Alake ya ce dole ne Nijeriya ta bunkasa tattalin arzikinta musamman bangaren masana’antu domin samun damar taka muhimmiyar rawa a yankin Afirka da bangaren ciniki (AFCFTA).

Ya ce duk da cewa AFCFTA ba ita ce mafita ga tattalin arzikin Nijeriya ba, amma ya yi watsi da cewa kasar nan za ta iya samun tagomashi daga gare ta ta hanyar tallafawa ci gaban masana’antu.

Mista Alake ya bukaci gwamnatocin kasashen Afirka ta Yamma da su gyara matsalolin da ke kawo cikas ga aiwatar da ka’idojin kungiyar ECOWAS, inda ya bayyana cewa har yanzu harkokin kasuwanci a kasashen yammacin Afirka na samun koma baya.

Ya bayar da shawarar inganta iyakokin, tashoshin jiragen ruwa a nahiyar domin samun bunkasar tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaDangoteTaroTattalin ArzikiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Yi Walimar Saukar Alkur’ani Ta ‘Yar Abba El-Mustapha

Next Post

Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

16 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

17 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

1 day ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

1 day ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

1 day ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

1 day ago
Next Post
Dawowar Ta’addanci Ta Sake Jefa Sakkwatawa Da Zamfarawa Cikin Zullumi

Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.