• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Murnar Zagayowar Ranar Kafuwar Kasar Sin: Bikin Bana Na Daban Ne

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Sin

Bikin bana na ranar kafuwar kasar Sin karo na 76 na daban ne bisa yadda ya zo lokaci guda da bikin tsakiyar kaka, wato biki na biyu mafi girma a kasar Sin. Don haka ya kunshi bangaren kishin kasa da na sake haduwar iyali don yaukaka zumunci da kauna, inda za a kwashi tsawon kwanaki takwas ana more hutu a kasar.

 

Baya ga bukukuwa, ranar kafuwar kasar Sin ta shekarar 2025 ta zama wani muhimmin lokaci na zamanantarwar kasar da nasarorinta a fagen kasa da kasa musamman a fannin kirkire-kirkire, bunkasa ci gaban bil’adama da kuma diflomasiyya.

  • PENGASSAN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Ta Fara
  • Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

Taken bikin ranar a bana “Zamanantarwa domin al’umma” ya nuna cewa, ci gaba ba wai kawai a gudanar da gine-gine da kere-kere ba ne, dole ne a yi ta fuskar da zai shafi inganta rayuwa, da kiyaye al’adu, da kuma tunanin makomar gaba.

 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Kyawawan sakamakon da aka samu a tsarin ci gaban kasa na shekaru biyar-biyar wanda a bana ake kammala karo na 14, sun nuna muhimmancin da ake bai wa rayuwar al’umma. A halin yanzu kasar Sin tana alfahari da tsarin kula da samar da ruwa mafi girma a duniya, inda ta mallaki manyan tafkunan adana ruwa fiye da 95,000, da manyan ayyuka 200 na janyo ruwa zuwa yankunan da ba su da shi domin aikin gona da inganta rayuwa a birane. Zuba jarin kasar a bangaren bincike da samarwa (R&D) ya karu da kashi 50%, wanda hakan ya haifar da samun nasarorin kimiyya masu yawa a cikin kasa har ma da duniya.

 

Bangaren samar da ci gaba mara gurbata muhalli na samun habaka cikin hanzari, inda karfin samar da sabon makamashi ya ninka zuwa fiye da kilowatts biliyan 2. Walwalar al’umma na kara habaka ta fuskar kiwon lafiya da sauran muhimman harkokin rayuwa ciki har da kula da ‘yan fansho da kaso 95%, kuma tattalin arzikin kasar a matsakaicin mizanin shekara-shekara yana bunkasa da akalla 5.5% tare da ba da gudummawar kusan kaso 30% na ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

 

Kazalika, bikin na bana ya zo a shekarar da kasar Sin ta kara azamar sauke nauyin da ke wuyarta a fagen kasa da kasa bisa muhimmiyar shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da shugaba Xi Jinping ya gabatar, gabanin taron cika shekaru 80 da kafuwar MDD. Wannan shawara tare da sauran muhimmai guda uku da shugaba Xi ya gabatar a baya, ba manufofi ba ne kawai, sun kasance sauye-sauye na falsafa da ke kunshe a cikin hikimar “samar da al’ummar duniya mai makoma ta bai-daya”.

 

Yayin da tsoffin tsare-tsaren da kasashen yammacin duniya suka kakaba wa duniya ke fuskantar hisabi, shawarwarin da kasar Sin ta bayar sun kawo mafita a kan yadda za a dama da bangarori masu yawa maimakon babakeren bangare guda, da yadda ko wace al’umma za ta iya tsara tafarkinta, tare da karfafa mutunta juna da samun ci gaba mai gamewa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Next Post
Masana’antar AI Ta Kasar Sin Ta Samu Habaka Da Kamfanoni Fiye Da 5300

Masana'antar AI Ta Kasar Sin Ta Samu Habaka Da Kamfanoni Fiye Da 5300

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.