ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

by Sulaiman
7 months ago
Sin

Kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta Sin wato JKS ya gudanar da taron manema labarai da safiyar yau Jumma’a, don fayyace ruhin cikakken zama na hudu na kwamitin kolin na 20 a birnin Beijing na Sin.

 

Yayin taron, mataimakin darektan ofishin kula da harkokin yau da kullum na hukumar kula da harkokin kudi da tattalin arziki ta kwamitin kolin JKS, kana darektan hukumar kula da aikin gona ta kwamitin kolin Han Wenxiu, ya ce, shawarwarin da kwamitin kolin JKS ya gabatar na tsara shirin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma na shekaru biyar-biyar karo na 15, wanda babban taron ya zartas da shi, ya fayyace manyan manufofin ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’umma da za a samu a fannoni bakwai, cikin shekaru biyar masu zuwa.

ADVERTISEMENT
  • Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu
  • Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Na farko, ana sa ran ganin ci gaba mai inganci a kasar zai haifar da kyawawan sakamako. Na biyu, za a inganta yanayin dogaro da kai a fannin kimiyya da fasaha. Na uku, za a sami sabbin ci gaba wajen zurfafa gyare-gyare a bangarori daban daban. Na hudu, za a inganta fannin al’adu da wayewar kan al’umma matuka. Na biyar, za a ci gaba da kyautata rayuwar jama’a. Na shida, za a sami babban ci gaba a fannin kare da inganta muhallin kasar. Na bakwai kuma, za a kara karfafa tsaron kasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Bugu da kari, Han ya ce, zamanantar da aikin gona da raya yankunan karkara tana da matukar muhimmanci a cikin aikin zamanantarwa irin ta kasar Sin, saboda haka ya kamata a ba wannan bangare fifiko. Ya ce shawarwarin da kwamitin kolin JKS ya gabatar na jaddada bukatar mai da raya harkoki masu alaka da aikin gona da raya yankin karkara da kyautata rayuwar manoma, a matsayin abu mai matukar muhimmanci, da tabbatar da bunkasar birane da yankin karkara na bai daya, da kuma hanzarta wajen inganta karfin kasar a fannin raya aikin gona.

 

A yayin taron, direktan hukumar raya kasa da gyare-gyare ta kasar Sin, Mr. Zheng Shanjie ya bayyana cewa, “kirkira da habaka sabbin abubuwa” na nufin habakawa da karfafa sabbin masana’antu da masana’antun da za su bullo a nan gaba. A shekarar 2024, tattalin arzikin “sabbin abubuwa uku” (wato sabbin masana’antu da sabbin nau’o’in cinikayya da sabbin hanyoyin kasuwanci) na Sin ya kai kashi 18% cikin alkaluman GDP na kasar. Shawarar da kwamitin tsakiyar JKS ya gabatar game da shiri na 15 na ci gaban tattalin arziki da zamantakewa na shekaru biyar-biyar, ya yi kira da a kirkiro sabbin masana’antu masu muhimmanci, da gaggauta habaka gungun masana’antu masu muhimmanci kamar sabbin makamashi, sabbin kayayyakin aiki da bangaren harkokin sararin samaniya, da tattalin arzikin kasa, wanda zai haifar da kasuwanni da darajarsu za ta wuce Yuan tiriliyan 1. Kazalika shawarar ta yi kira da a shirya da wuri don kafa masana’antu na nan gaba, kamar ta fasahar lissafi ta quantum da kirkirar kayayyakin halitta da makamashin hydrogen da na nukiliya da hada kwakwalwar bil adam da na’ura da fasahar wayar hannu na zamani, da sauransu, wadanda za su zama sabbin hanyoyin habaka tattalin arziki. Wadannan masana’antu a shirye suke don kara karfi wajen kokarin habaka masana’antar fasaha a nan kasar Sin, a cikin shekaru 10 masu zuwa.

 

Ministan kula da cinikayya na kasar Sin Wang Wentao ya bayyana a yau Juma’a cewa, kasar za ta fadada bude kofarta ga kasashen waje yayin aiwatar da shirin raya kasa na shekaru 5, na 15.

 

Wang Wentao ta kara da cewa, tsakanin shekarar 2026 zuwa ta 2030, za a yi kokarin fadada ba da damar shiga kasuwa da bangarorin da za a kara bude wa kofa, a bangaren bayar da hidimomi. Ministan ya ce wadannan na cikin shawarwarin da kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya gabatar wajen tsara shirin na 15 dake da burin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin, wanda aka amince da shi yayin zama na 4 na kwamitin kolin da aka kammala jiya Alhamis.

 

A cewarsa, sauran manyan ayyuka sun hada da raya sabbin harkokin cinikayya da samar da karin hanyoyin zuba jari tsakanin Sin da kasa da kasa da kuma daukaka hadin gwiwar shawarar Ziri Daya da Hanya Daya. (Safiyah Ma, Amina Xu, Fa’iza Muhammad Mustapha)

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta'addanci

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.