An samu rahoton hatsarin wani Kwalekwale wanda ya kife da ‘yan kasuwar jihar Neja bayan sun gama cin kasuwar garin Yauri da ke karamar hukumar Yelwa/Yauri a Jihar Kebbi.
Lamarin wanda ya afku a yammacin ranar Talata, an bayyana cewa, Kwalekwalen yana dauke da ‘yan kasuwa daga garin Hikiya da ke cikin karamar Hukumar Rohiya a jihar Neja.
- Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
- Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
Amma rahotannin sun nuna cewa, Mutane hudu sun bace a ruwan, an tsamo gawarwaki uku, sannan ana ci gaba da aikin ceto, kamar yadda kungiyar Red Cross a garin na Yauri ta bayyana.
Aiki ceton, ya samu hadin gwiwar kungiyoyin ceto da suka hada da Red Cross da Hukumar Kula da Ruwan Kogin (NIWA) da jama’ar garin Yauri.
A ranar Laraba, an yi jana’izar Mutane uku, a garin Hikiya da ke karamar hukumar Rohiya a jihar Neja.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp