• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 10 Sun Mutu Bayan Shan Shayin Gadagi A Wajen Daurin Aure A Kano

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 10 Sun Mutu Bayan Shan Shayin Gadagi A Wajen Daurin Aure A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane 10 ne aka ruwaito cewa sun mutu, inda wasu kuma da dama, aka kwantar da su a asibiti bayan da suka sha shayin gadagi wanda ake zargin an hada shi ne da wani ganyen shayin Zakami.

Mutanen sun sha shayin ne, a taron wani biki a Jihar Kano.

  • Buhari Ya Nada Sabon Mai Ba Da Shawara Kan Sha’anin Tsaro
  • Ma’aikatan Filato Sun Fara Yajin Aiki Kan Rashin Biyan Su Albashi

Zakami dai, na dauke da wani sanadarin da ke sanya wa wanda ya sha kuzari.

Lamarin ya auku ne a ranar Talata a unguwar Sheka da ke a karamar hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Daya daga cikin ganau, Sanusi Yahaya wanda kuma babban yaya ne ga amaryar da aka daura wa auren, ya bayyana cewa, ana zargin ana hada shayin da kwaya da kuma ganyen Zakamin.

Labarai Masu Nasaba

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

Ya ce, abin kusan ya zama jiki, musamman ga masu ta’ammali da kayan maye da ke yin amfani da shi a lokacin bukukuwa.

A cewarsa, suna dafa shayin kuma ba su san adadin kwayar da ke cikin shayin ba, inda hakan ya sa wasu suka yi watsi da shayin wasu kuma suka matsa sai sun sha shayin bisa cewarsu kwakwalwarsu za ta iya dauka.

Ya ci gaba da cewa, bayan sun sha shayin ne, sai mutum biyu suka fara mutuwa, wasu kuma suka farfado, inda kuma garzaya da wasu asibiti.

Shi ma wani ganau, Abdullahi Muhammad, ya bayyana cewa, a ranar Talata mutum bakwai sun mutu, inda aka danganta mutuwar da shan shayin.

A cewarsa, ba mu san yawan adadin wadanda suka mutu ba, amma da safiyar Talatar an tabbatar da mutuwar mutane bakwai, inda ya ce, wasun ma ba wanda ya gayyace su zuwa daurin auren sun zo ne kawai don su fake da daurin, don su sha kayan maye.

Ba a dai iya jin ta bakin angon ba, don jin ta nasa bangaren kan lamarin.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa, rundunar da kuma caji ofis na yankin da lamarin ya auku, ba su samu rahoton faruwar lamarin ba.

Amma ya yi alkwarin yin karin haske da zarar ya samu rahoton faruwar lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daurin AureGadagikanoShayiShekaZakami
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Nada Sabon Mai Ba Shi Shawara Kan Sha’anin Tsaro

Next Post

Za A Tafka Mamakon Ruwan Sama A Arewa A Kwanaki Masu Zuwa —NiMet

Related

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

28 minutes ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 hour ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

10 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

13 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

16 hours ago
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

18 hours ago
Next Post
Za A Tafka Mamakon Ruwan Sama A Arewa A Kwanaki Masu Zuwa —NiMet

Za A Tafka Mamakon Ruwan Sama A Arewa A Kwanaki Masu Zuwa —NiMet

LABARAI MASU NASABA

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.