• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 547,774 Suka Cike Aikin Dansanda, Mako 1 Ya Rage A Rufe Shafin Daukar Aikin

by Muhammad
2 years ago
Mutum

Hukumar ‘Yansanda ta fitar da sanarwa cewa mako guda ya rage kafin ta rufi shafin daukar sababbin ‘Yansanda a fadin Nijeriya.

Yanzu haka shafin ya samu masu neman aiki su kimanin mutum dubu dari biyar da bakwai, da dari bakwai da saba’in da hudu (547,774) a matsayin masu neman aiki Dan sanda a rundunar ‘yan sandan Nijeriya gabanin rufe shafin a ranar Lahadi mai zuwa, 26 ga Nuwamba, 2023 wanda zai cika makonni 6 na na wa’adin da hukumar ta sanya.

  • Yadda ‘Yansanda Suka Min Duka Kamar Dan Ta’adda – Shugaban NLC
  • A Sake Fasalin Rundunar ‘Yansandan Nijeriya

An buɗe shafin a ranar 15 ga Oktoba, 2023, makonni biyar da suka gabata.

Daga cikin 547,774 masu neman aiki, 358,900 sun yi nasara kuma sun cancanci zuwa zagaye na gaba na tsarin daukar ma’aikata wanda ya hada da yanayin kirar jikinsu da lafiyarsu da ingancin takaddunsu bayanansu.

An yi cire mutane akalla sama da 84,606 na masu neman aikin wadanda shekarunsu na haihuwa suke tsakanin shekaru 18 zuwa 25, inda aka fitar da su.

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Jihar Kaduna ce Jiha ta farko a matsayin jihar da ta fi kowacce yawan masu nema aikin da mutum 40,272 sai Jhar Anambra wadda take a matsayin Jihana karshe da mutum 1664.

Kazalika Jihar Adamawa ce ta biyu da mutum 36,398, sai Jihar Borno da ta zo ta uku da mutum 32,048.

Jihar Benue na da 31,122 wadda ita ce a matsayin ta hudu, sai Jihar Katsina a matsayi na biyar mai mutum 30,202, sai Jihar Bauchi mai mutum 30,604 a matsayin ta 6 yayin da Jihar Kano ke bite mata a matsayin Jiha ta 7 da mutum 30,004.

Sauran Jihohin sun hada da Jihar Ebonyi mai mutum 2132, sai Jihar Legas mai mutane 2324. Jihar Bayelsa na da 2651 yayin da Abia ke da 2796.

Sufeto Janar na ‘yan sanda mai ritaya, Dr. Solomon Arase, ya bayyana jin dadinsa da yawan adadin manema aikin da aka samu da suka nuna sha’awar neman aiki na ‘yan sandan Nijeriya.

Tsohon Sifeton ya ce, Hukumar za ta yi iya bakin kokarinta don ganin daukar ma’aikatan an yi bisa ka’idojin da aka ayyana tare da duba cancanta da kuma adalci a yayin gudanar da aikin kamar yadda sanarwar Kakakin rundunar na kasa, Ikechukwu Ani, ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, 19 ga Watan Nuwambar 2023 da muke ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Next Post
An Tsinci Gawar Mutum 9 Da Hatsarin Kwale-kwale Ya Rutsa Da Su A Jihar Neje – NSEMA

An Tsinci Gawar Mutum 9 Da Hatsarin Kwale-kwale Ya Rutsa Da Su A Jihar Neje – NSEMA

LABARAI MASU NASABA

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.