• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke kula da harkokin jin kai, (UNOCHA) ya ce, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 7.9 ne suke cikin halin neman taimakon gaggawa da na jin kai a jihohin Borno, Adamawa da kuma Yobe.

 

Jihohi uku sun sha fama da matsalolin rashin tsaro, musamman na Boko Haram, wanda ya janyo hallaka dubban mutane da tursasa wa wasu miliyoyi yin gudun hijira na dole tsawon shekaru kusan ashirin.

  • An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe
  • Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto

A yayin bikin tunawa da ranar jin kai ta duniya na wannan shekarar da ya gudana a ranar Litinin a Yola, UNOCHA da take baje kolin kiddigar ta nuna cewa adadin mutum miliyan 3.9 ne suke neman tallafi a Jihar Borno, yayin da Jihar Adamawa ke da adadin mutum miliyan 2.2, inda ita kuma Jihar Yobe ke da adadin mutum miliyan 1.8 ke tsananin bukatar agajin gaggawa.

 

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

Kiddigar ta kuma nuna cewa mata da yara sun kunshi kaso 80 cikin 100 na wannan adadin masu neman abinci mai gina jiki.

 

Ko-odinatan shirin a Nijeriya, Mohamed Malick Fall, ya nanata matsalar karancin abincin mai gina jiki a shiyyar, kaso uku ne kawai na cikin dala miliyan 306 da aka bukata domin magance matsalar ne aka samu zuwa yanzu.

 

“Dole mu hada karfi da karfe mu yi aikin jin kai domin dakile wahalar da suke sha,” Fall ya bukata.

 

A Jihar Adamawa lamuran sun kara tabarbarewa ne sakamakon kwararowar ‘yan gudun hijira 33,000 daga kasar Kamaru, wadanda suka tsere wa hare-haren kungiyoyin ‘yan bindiga, a cewar hukumar samar da agajin gaggawa ta Jihar Adamawa (ADSEMA).

 

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, da ya samu wakilcin mataimakinsa, Farfesa Kaletapwa Farauta, ya jaddada muhimmancin hada karfi da karfi domin tunkarar matsalar.

 

Ya ce dole ne a ci gaba da aikata kyawawan abubuwan da za su kasance na jin kai da tausayin wadanda suke cikin halin bukatar hakan domin kyautata rayuwa a kowani lokaci.

 

Shugaban Ofishin Majalisar Dinkin Duniyan da ke Damaturu, Dabid Lubari Lominyo shi ne ya sanar da wannan yayin da ke ganawa da ‘yan jarida kan ranar jin kai ta duniya. Bayanan sun fito ne daga rahoton ofishin sakatare janar na majalisar dinkin duniya na 2024 kan kare fafaren hula daga rikice-rikicen ta’addanci.

 

Lominyo ya bayyana cewar kare hakkin fafaren hula shi ne babban abun da suka sanya a gaba domin karesu daga hare-haren ‘yan bindiga masu aikata ta’addanci. Ya lura kan cewa hare-haren Boko Haram ya tuguza tattalin arziki sosai.

 

Ya roki dukkanin masu hannu da masu ruwa da tsaki da hukumomin tsaro da su kara himma da azama wajen ganin rayukan fafaren hula sun samu kariya da kiyayewa a kowani lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe

Next Post

Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Related

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
Labarai

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

57 minutes ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

6 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

7 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

8 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

9 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

23 hours ago
Next Post
Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.