• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
UNOCHA

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke kula da harkokin jin kai, (UNOCHA) ya ce, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 7.9 ne suke cikin halin neman taimakon gaggawa da na jin kai a jihohin Borno, Adamawa da kuma Yobe.

 

Jihohi uku sun sha fama da matsalolin rashin tsaro, musamman na Boko Haram, wanda ya janyo hallaka dubban mutane da tursasa wa wasu miliyoyi yin gudun hijira na dole tsawon shekaru kusan ashirin.

  • An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe
  • Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto

A yayin bikin tunawa da ranar jin kai ta duniya na wannan shekarar da ya gudana a ranar Litinin a Yola, UNOCHA da take baje kolin kiddigar ta nuna cewa adadin mutum miliyan 3.9 ne suke neman tallafi a Jihar Borno, yayin da Jihar Adamawa ke da adadin mutum miliyan 2.2, inda ita kuma Jihar Yobe ke da adadin mutum miliyan 1.8 ke tsananin bukatar agajin gaggawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Kiddigar ta kuma nuna cewa mata da yara sun kunshi kaso 80 cikin 100 na wannan adadin masu neman abinci mai gina jiki.

 

Ko-odinatan shirin a Nijeriya, Mohamed Malick Fall, ya nanata matsalar karancin abincin mai gina jiki a shiyyar, kaso uku ne kawai na cikin dala miliyan 306 da aka bukata domin magance matsalar ne aka samu zuwa yanzu.

 

“Dole mu hada karfi da karfe mu yi aikin jin kai domin dakile wahalar da suke sha,” Fall ya bukata.

 

A Jihar Adamawa lamuran sun kara tabarbarewa ne sakamakon kwararowar ‘yan gudun hijira 33,000 daga kasar Kamaru, wadanda suka tsere wa hare-haren kungiyoyin ‘yan bindiga, a cewar hukumar samar da agajin gaggawa ta Jihar Adamawa (ADSEMA).

 

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, da ya samu wakilcin mataimakinsa, Farfesa Kaletapwa Farauta, ya jaddada muhimmancin hada karfi da karfi domin tunkarar matsalar.

 

Ya ce dole ne a ci gaba da aikata kyawawan abubuwan da za su kasance na jin kai da tausayin wadanda suke cikin halin bukatar hakan domin kyautata rayuwa a kowani lokaci.

 

Shugaban Ofishin Majalisar Dinkin Duniyan da ke Damaturu, Dabid Lubari Lominyo shi ne ya sanar da wannan yayin da ke ganawa da ‘yan jarida kan ranar jin kai ta duniya. Bayanan sun fito ne daga rahoton ofishin sakatare janar na majalisar dinkin duniya na 2024 kan kare fafaren hula daga rikice-rikicen ta’addanci.

 

Lominyo ya bayyana cewar kare hakkin fafaren hula shi ne babban abun da suka sanya a gaba domin karesu daga hare-haren ‘yan bindiga masu aikata ta’addanci. Ya lura kan cewa hare-haren Boko Haram ya tuguza tattalin arziki sosai.

 

Ya roki dukkanin masu hannu da masu ruwa da tsaki da hukumomin tsaro da su kara himma da azama wajen ganin rayukan fafaren hula sun samu kariya da kiyayewa a kowani lokaci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Next Post
Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.