ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
UNOCHA

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke kula da harkokin jin kai, (UNOCHA) ya ce, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 7.9 ne suke cikin halin neman taimakon gaggawa da na jin kai a jihohin Borno, Adamawa da kuma Yobe.

 

Jihohi uku sun sha fama da matsalolin rashin tsaro, musamman na Boko Haram, wanda ya janyo hallaka dubban mutane da tursasa wa wasu miliyoyi yin gudun hijira na dole tsawon shekaru kusan ashirin.

ADVERTISEMENT
  • An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe
  • Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto

A yayin bikin tunawa da ranar jin kai ta duniya na wannan shekarar da ya gudana a ranar Litinin a Yola, UNOCHA da take baje kolin kiddigar ta nuna cewa adadin mutum miliyan 3.9 ne suke neman tallafi a Jihar Borno, yayin da Jihar Adamawa ke da adadin mutum miliyan 2.2, inda ita kuma Jihar Yobe ke da adadin mutum miliyan 1.8 ke tsananin bukatar agajin gaggawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Kiddigar ta kuma nuna cewa mata da yara sun kunshi kaso 80 cikin 100 na wannan adadin masu neman abinci mai gina jiki.

 

Ko-odinatan shirin a Nijeriya, Mohamed Malick Fall, ya nanata matsalar karancin abincin mai gina jiki a shiyyar, kaso uku ne kawai na cikin dala miliyan 306 da aka bukata domin magance matsalar ne aka samu zuwa yanzu.

 

“Dole mu hada karfi da karfe mu yi aikin jin kai domin dakile wahalar da suke sha,” Fall ya bukata.

 

A Jihar Adamawa lamuran sun kara tabarbarewa ne sakamakon kwararowar ‘yan gudun hijira 33,000 daga kasar Kamaru, wadanda suka tsere wa hare-haren kungiyoyin ‘yan bindiga, a cewar hukumar samar da agajin gaggawa ta Jihar Adamawa (ADSEMA).

 

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, da ya samu wakilcin mataimakinsa, Farfesa Kaletapwa Farauta, ya jaddada muhimmancin hada karfi da karfi domin tunkarar matsalar.

 

Ya ce dole ne a ci gaba da aikata kyawawan abubuwan da za su kasance na jin kai da tausayin wadanda suke cikin halin bukatar hakan domin kyautata rayuwa a kowani lokaci.

 

Shugaban Ofishin Majalisar Dinkin Duniyan da ke Damaturu, Dabid Lubari Lominyo shi ne ya sanar da wannan yayin da ke ganawa da ‘yan jarida kan ranar jin kai ta duniya. Bayanan sun fito ne daga rahoton ofishin sakatare janar na majalisar dinkin duniya na 2024 kan kare fafaren hula daga rikice-rikicen ta’addanci.

 

Lominyo ya bayyana cewar kare hakkin fafaren hula shi ne babban abun da suka sanya a gaba domin karesu daga hare-haren ‘yan bindiga masu aikata ta’addanci. Ya lura kan cewa hare-haren Boko Haram ya tuguza tattalin arziki sosai.

 

Ya roki dukkanin masu hannu da masu ruwa da tsaki da hukumomin tsaro da su kara himma da azama wajen ganin rayukan fafaren hula sun samu kariya da kiyayewa a kowani lokaci.

UNOCHA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
UNOCHA
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.