ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
UNOCHA

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke kula da harkokin jin kai, (UNOCHA) ya ce, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 7.9 ne suke cikin halin neman taimakon gaggawa da na jin kai a jihohin Borno, Adamawa da kuma Yobe.

 

Jihohi uku sun sha fama da matsalolin rashin tsaro, musamman na Boko Haram, wanda ya janyo hallaka dubban mutane da tursasa wa wasu miliyoyi yin gudun hijira na dole tsawon shekaru kusan ashirin.

ADVERTISEMENT
  • An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe
  • Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto

A yayin bikin tunawa da ranar jin kai ta duniya na wannan shekarar da ya gudana a ranar Litinin a Yola, UNOCHA da take baje kolin kiddigar ta nuna cewa adadin mutum miliyan 3.9 ne suke neman tallafi a Jihar Borno, yayin da Jihar Adamawa ke da adadin mutum miliyan 2.2, inda ita kuma Jihar Yobe ke da adadin mutum miliyan 1.8 ke tsananin bukatar agajin gaggawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Kiddigar ta kuma nuna cewa mata da yara sun kunshi kaso 80 cikin 100 na wannan adadin masu neman abinci mai gina jiki.

 

Ko-odinatan shirin a Nijeriya, Mohamed Malick Fall, ya nanata matsalar karancin abincin mai gina jiki a shiyyar, kaso uku ne kawai na cikin dala miliyan 306 da aka bukata domin magance matsalar ne aka samu zuwa yanzu.

 

“Dole mu hada karfi da karfe mu yi aikin jin kai domin dakile wahalar da suke sha,” Fall ya bukata.

 

A Jihar Adamawa lamuran sun kara tabarbarewa ne sakamakon kwararowar ‘yan gudun hijira 33,000 daga kasar Kamaru, wadanda suka tsere wa hare-haren kungiyoyin ‘yan bindiga, a cewar hukumar samar da agajin gaggawa ta Jihar Adamawa (ADSEMA).

 

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, da ya samu wakilcin mataimakinsa, Farfesa Kaletapwa Farauta, ya jaddada muhimmancin hada karfi da karfi domin tunkarar matsalar.

 

Ya ce dole ne a ci gaba da aikata kyawawan abubuwan da za su kasance na jin kai da tausayin wadanda suke cikin halin bukatar hakan domin kyautata rayuwa a kowani lokaci.

 

Shugaban Ofishin Majalisar Dinkin Duniyan da ke Damaturu, Dabid Lubari Lominyo shi ne ya sanar da wannan yayin da ke ganawa da ‘yan jarida kan ranar jin kai ta duniya. Bayanan sun fito ne daga rahoton ofishin sakatare janar na majalisar dinkin duniya na 2024 kan kare fafaren hula daga rikice-rikicen ta’addanci.

 

Lominyo ya bayyana cewar kare hakkin fafaren hula shi ne babban abun da suka sanya a gaba domin karesu daga hare-haren ‘yan bindiga masu aikata ta’addanci. Ya lura kan cewa hare-haren Boko Haram ya tuguza tattalin arziki sosai.

 

Ya roki dukkanin masu hannu da masu ruwa da tsaki da hukumomin tsaro da su kara himma da azama wajen ganin rayukan fafaren hula sun samu kariya da kiyayewa a kowani lokaci.

UNOCHA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy
UNOCHA
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Next Post
Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.