Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, ya tabbatar da mubaya’arsa ga Atiku Abubakar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023.
BBC ta rawaito cewa, har yanzu dai Wike ya ce yana nan a kan bakarsa cewar dole shugaban jam’iyyar ta Peoples Democratic Party Iyorchia Ayu ya sauka daga muƙaminsa.
- Kwamitin Amintattu Na PDP Ya Gana Da Wike Kan Rikicin Jam’iyyar
- 2023: Atiku Ya Karyata Batun Zai Goyi Bayan Wike A Zaben 2027
Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Wike ya tabbatar da haka ne a wani taro da ya yi da ‘ƴan takarar jam’iyyar na jihar Rivers a mataki daban-daban, a garin Port Harcourt, a daren Alhamis.
Wike ya ce ana iyakar bakin ƙoƙari wajen ganin an warware rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar sai dai wasu ƴan-ba-ni na-iya ne suke kawo cikas.
Ya ce “An gama zaɓen fitar da gwani. Na ce a cire ɗan takarar shugaban ƙasa ne?
Ko na ce a cire ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa? To mene ne kuma ake ba ni haƙuri a kai?
“Abin da nake cewa shi ne tunda kun samu ɗan takarar shugaban ƙasa to ku ba mu muƙamin shugaban jam’iyya.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp