• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

by Sulaiman
3 hours ago
in Labarai
0
Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana jin daɗinsa na biyan bashin Naira Biliyan 13,944,039,204.64 da aka riƙe wa ’yan fansho a Zamfara tun daga shekarar 2011 zuwa 2023.

 

A ranar Talatar da ta gabata ne gwamnan ya ƙaddamar da kwamitin aiwatar da ayyukan fansho tare da karbar rahoto daga kwamitocin haɗin gwiwa kan biyan bashin kuɗaɗen garatuti da aka yi a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu
  • Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, warware tarin bashin kuɗaɗen guratuti da fansho da aka tara daga shekarar 2011 zuwa 2023 na ɗaya daga cikin manyan nasarorin da gwamnatin ta samu.

 

Labarai Masu Nasaba

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Sanarwar ta ƙara da cewa mutane 3,824 da suka yi aiki a ƙarƙashin gwamnatin jiha sun samu N7,960,162,598.64, yayin da 4,833 daga ƙarananan hukumomi aka tantance kuma an biya su N5,983,876,606 a matsayin garatuti. A jimlace, an biya N13,944,039,204.64 a matsayin kuɗaɗen garatuti.

Zamfara

Gwamna Lawal bayan ya karbi rahoton ya ce gwamnatinsa ta ba da fifiko wajen daidaita biyan haƙƙoƙin ma’aikatan gwamnati, musamman waɗanda suka yi ritaya bayan shekaru 35 suna aiki kuma suka kai shekaru 60.

 

“Gwamnatinmu ta gaji sama da Naira Biliyan 13 a matsayin bashin kuɗaɗen garatuti na waɗanda suka yi ritaya daga Jiha da Ƙananan Hukumomin daga 2011 zuwa 2023, jinkirin ya jawo wahalhalu, kuma wasu da suka yi ritaya sun mutu su na jiran a biya su haƙƙin su, Allah ya jiƙan su da rahama.

 

“Don magance wannan rashin adalci, mun kafa kwamitoci guda biyu domin su duba tare da ba da shawarar biyan duk wata garatuti da aka riƙe wa waɗanda suka yi ritaya daga Jiha da Ƙananan Hukumomi, a lokacin da muka karbi ragamar mulki shekaru biyu da suka wuce, duk da ƙalubalen tattalin arziki da zamantakewa, mun biya ma’aikatan gwamnati albashin watanni uku tare da biyan su alawus-alawus. Mun kuma daidaita alawus-alawus na alƙalai da ma’aikatan shari’a na tsawon shekaru.

 

“Mun daidaita duka waɗannan abubuwa. Lokacin da muka karbi mulki, mafi ƙarancin albashi a jihar ya kasance Naira 7,000.00 ne kacal, mafi ƙarancin albashi na N30,000, wanda aka amince da shi a shekarar 2019, gwamnatin da ta shuɗe ba ta taba aiwatar da shi ba, saboda sanin nauyin da ya rataya a wuyanmu, mun aiwatar da mafi ƙarancin albashi na N30,000.00 nan take.

 

“Bayan mun duba tsarin mafi ƙarancin albashin da ya ƙaru daga N30,000 zuwa N70,000.00 a watan Yulin 2024, mun aiwatar da sji bayan duk matakan da suka dace, ta yadda a cikin shekaru biyu na mulki, mun ƙara mafi ƙarancin albashi a jihar daga N7,000.00 zuwa N70,000.00.

 

“Bugu da ƙari kuma, mun bullo da kuma aiwatar da hanyoyin kyautata wa ma’aikata a yayin bukukuwan Sallah da kuma ƙarin garabasar albashin ƙarshen shekara, wanda aka fi sani da albashin wata na 13 ga duk ma’aikatan gwamnati da masu riƙe da muƙaman gwamnati, ba a taba yin hakan ba a tarihin jihar.

 

“Sakamakon biyan kuɗaɗen garatuti ya ƙara wa ma’aikata kwarin gwiwa tare da dawo da amincewar jama’a kan harkokin mulki, za mu ci gaba da tabbatar da samar da kuɗaɗen fansho cikin gaggawa, domin yin hakan, gwamnatin jihar a shirye take ta haɗa gwiwa da ƙungiyoyin ‘yan fansho domin tafiya daidai da sauye-sauyen da muka yi.

Zamfara

“Yayin da nake samun wannan rahoton, ina so in yaba wa ƙoƙari da jajircewar ‘yan kwamitin, wannan ba abu ne mai sauƙi ba, ina sane da ƙalubalen da ‘yan kwamitin suka fuskanta a yayin gudanar da aiki, ba yaba da jajircewarsu.

 

A yayin ƙaddamar da kwamitin aiwatar da ayyukan fansho, gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta tabbatar da yin garambawul a harkokin fansho na jiha da ƙananan hukumomi.

 

“Gwamnatina ta kafa wani kwamiti da zai duba ayyukan da suka gabata na hukumar fansho a jihar, kwamitin ya kammala aikinsa tare da bayar da shawarwari kan yadda za a ci gaba, wani bangare na shawarwarin shi ne kafa kwamitin aiwatar da ayyukan fansho.

 

“Don bin tsarin Ma’aikatar Shari’a, Hukumar Fansho ta Jiha, da duk masu ruwa da tsaki za su duba tare da sabunta dokar fansho ta Jihar Zamfara domin Majalisar Dokokin Jihar ta amince da ita cikin gaggawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Related

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe
Labarai

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

5 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

1 hour ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

3 hours ago
Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata
Labarai

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

4 hours ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

8 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

11 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe

July 9, 2025
An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025

July 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja

July 9, 2025
Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

July 9, 2025
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

July 9, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

July 9, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

July 9, 2025
Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal

July 9, 2025
Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

July 9, 2025
Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

Peter Obi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Aminu Dantata

July 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.