• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani – Manta

by Sulaiman and Muhammad Awwal Umar
3 years ago
in Labarai
0
Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani – Manta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar ‘yan banga a jihar Neja, Yarima Nasiru Manta yayi barazanar dakatar da aikin kungiyar na yaki da masu garkuwa da mutane da suka addabi mutanen karkara da hanyoyin jihar da ‘yan daba da suka addabi cikin garin Minna.

Shugaban ya bayyana hakan ne ga manema labarai jim kadan bayan rundunar ‘yan sanda ta sako shi bayan tsare shi kwana daya da yini daya a hedikwatar rundunar ‘yan sandan.

  • Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

Manta, ya cigaba da cewar wasu marasa kishin jiha ne suka kai korafi ga rundunar ‘yan sanda bisa zargin sa da cewa wai yana wuce gona-da-iri wajen tsare masu laifi sama da kwana uku.

Manta ya karyata zargin, Yace ba ma tsare masu laifi, domin kwamishinan ‘yan sandan da ya wuce CP Adamu Usman ne ya horar da mu bisa umurnin maigirma gwamna Abubakar Sani Bello saboda yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi jihar, mun samu nasara sosai da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro na tarwatsa sansanin ‘yan ta’adda masu garkuwa da jama’a, da kuma matasa ‘yan daba dake addaban mazauna cikin garin Minna.

Yarima Nasiru Manta, yace akwai wani dan siyasa da ke gidan gwamnatin jiha, da muka kama surukinsa cikin ‘yan daba, saboda kusancin sa da gwamnati sai ya garzaya hedikwatar rundunar ‘yan sanda ya baiwa kwamishinan ‘yan sanda rahoton karya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Ba tare da bata lokaci ba kwamishinan ‘yan sanda ya gayyace ni, nan take na amsa gayyatar sa, ba tare da bata lokaci ba ya umurci bangaren binciken laifuka na rundunar da su tsare ni.

Bayan an tsare ni kuma ‘yan daban suka cigaba da aika-aikar na su inda kwamishinan kananan hukumomi da masarautu da tsaron cikin gida, a daren washe gari cikin bacin rai ya umurci kwamishinan ‘yan sanda ya sake ni, ba tare da rubuta beli ko wani kwakkwaran bincike da safe aka sake ni.

Yanzu na umurci dukkanin mambobin mu da ke aiki tare da ni da su dakatar da aikin, mu bar ‘yan sanda su yi aikin su. Kila idan gwamna na son Aikin zai gayyaci dukkanin bangarorin dan jin bahasin abinda ya kai ga tsare ni. Ba sata na yi ba, laifina kawai kama masu laifi don suna da uwa a gindin murhu.

Ko a yammacin asabar zuwa wayewar lahadi ‘yan dabar sun farwa junansu a yankin Kwangila zuwa Limawa, da nan bangaren Limawa zuwa Obasanjo complex kuma na shaidawa yara cewar kar wanda ya fita.

Yunkurin jin ta bakin rundunar ‘yan sanda dai ya cutura, domin wayar kakakin rundunar ‘yan sandan ba ta zuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

Next Post

Sama Da Makarantu 2000 Sun Samu Tallafin Kudin Gyara A Kaduna

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da ÆŠansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

14 minutes ago
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115
Labarai

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

44 minutes ago
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja

2 hours ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da ÆŠansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 hours ago
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
Labarai

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

19 hours ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

23 hours ago
Next Post
Sama Da Makarantu 2000 Sun Samu Tallafin Kudin Gyara A Kaduna

Sama Da Makarantu 2000 Sun Samu Tallafin Kudin Gyara A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

May 31, 2025
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

May 31, 2025
Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

May 31, 2025
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

May 31, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

May 31, 2025
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.