ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani – Manta

by Sulaiman and Muhammad Awwal Umar
4 years ago
Manta

Shugaban kungiyar ‘yan banga a jihar Neja, Yarima Nasiru Manta yayi barazanar dakatar da aikin kungiyar na yaki da masu garkuwa da mutane da suka addabi mutanen karkara da hanyoyin jihar da ‘yan daba da suka addabi cikin garin Minna.

Shugaban ya bayyana hakan ne ga manema labarai jim kadan bayan rundunar ‘yan sanda ta sako shi bayan tsare shi kwana daya da yini daya a hedikwatar rundunar ‘yan sandan.

  • Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

Manta, ya cigaba da cewar wasu marasa kishin jiha ne suka kai korafi ga rundunar ‘yan sanda bisa zargin sa da cewa wai yana wuce gona-da-iri wajen tsare masu laifi sama da kwana uku.

ADVERTISEMENT

Manta ya karyata zargin, Yace ba ma tsare masu laifi, domin kwamishinan ‘yan sandan da ya wuce CP Adamu Usman ne ya horar da mu bisa umurnin maigirma gwamna Abubakar Sani Bello saboda yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi jihar, mun samu nasara sosai da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro na tarwatsa sansanin ‘yan ta’adda masu garkuwa da jama’a, da kuma matasa ‘yan daba dake addaban mazauna cikin garin Minna.

Yarima Nasiru Manta, yace akwai wani dan siyasa da ke gidan gwamnatin jiha, da muka kama surukinsa cikin ‘yan daba, saboda kusancin sa da gwamnati sai ya garzaya hedikwatar rundunar ‘yan sanda ya baiwa kwamishinan ‘yan sanda rahoton karya.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ba tare da bata lokaci ba kwamishinan ‘yan sanda ya gayyace ni, nan take na amsa gayyatar sa, ba tare da bata lokaci ba ya umurci bangaren binciken laifuka na rundunar da su tsare ni.

Bayan an tsare ni kuma ‘yan daban suka cigaba da aika-aikar na su inda kwamishinan kananan hukumomi da masarautu da tsaron cikin gida, a daren washe gari cikin bacin rai ya umurci kwamishinan ‘yan sanda ya sake ni, ba tare da rubuta beli ko wani kwakkwaran bincike da safe aka sake ni.

Yanzu na umurci dukkanin mambobin mu da ke aiki tare da ni da su dakatar da aikin, mu bar ‘yan sanda su yi aikin su. Kila idan gwamna na son Aikin zai gayyaci dukkanin bangarorin dan jin bahasin abinda ya kai ga tsare ni. Ba sata na yi ba, laifina kawai kama masu laifi don suna da uwa a gindin murhu.

Ko a yammacin asabar zuwa wayewar lahadi ‘yan dabar sun farwa junansu a yankin Kwangila zuwa Limawa, da nan bangaren Limawa zuwa Obasanjo complex kuma na shaidawa yara cewar kar wanda ya fita.

Yunkurin jin ta bakin rundunar ‘yan sanda dai ya cutura, domin wayar kakakin rundunar ‘yan sandan ba ta zuwa.

Manta
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Manta
Muhammad Awwal Umar
+ posts Bio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Sama Da Makarantu 2000 Sun Samu Tallafin Kudin Gyara A Kaduna

Sama Da Makarantu 2000 Sun Samu Tallafin Kudin Gyara A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.