• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata Malamar Jami’ar Oyo da ke jihar Akwa Ibom, Misis Christiana Pam, ta ce domin samun abincin da za ta rayu a irin wannan lokacin da kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ke ci gaba da gudanar da yajin aiki, a yanzu haka ta rungumi sana’ar sayar da Dankalin Turawa domin samun abin kai wa baki. 

A ranar 14 ga watan Fabrairu ne kungiyar ASUU ta tsunduma yajin aikin makonni hudu a matsayin gargadi bisa bukatun da suke, daga bisa ta kara tsawaita yajin aikin zuwa wasu watanni biyu a ranar 14 ga watan Maris. Sannan ta sake sanar da wasu karin makonni 12 a ranar 9 ga watan Mayu.

  • Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo
  • Wasu Gwamnatocin Kasashe Sun Nanata Matsayinsu Na Tsaiwa Tsayin Daka Kan Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Yajin aikin kamar yadda kungiyar ta ce, ta shiga ne sakamakon kasa ciki mata alkawuran da suka yi da Gwamnatin tarayya dangane da wasu tilin bukatun da take da su.

A hirarta da majiyarmu bayan da hotunan ta suka karade kafafen sadarwar zamani da ke nunata tana sana’ar, Pam ta ce, ta shiga halin matsatsi na rashin kudi sakamakon ita sabuwar ma’aikaciya ce wacce ba ta samu damar tara kudade masu yawan da za ta iya rayuwa muddin yajin aikin ya jima ba.

“Lokacin da aka ayyana yajin aikin wata guda, na yi tsammanin cewa ba za a wuce wannan lokacin ba za a dawo. Na dauka cewa kungiyar ASUU da gwamantin za su samu fahimtar juna kan bukatun ASUU, kwatsam sai kuma hakan ba ta faru ba, a takaice dai aka tsawaita yajin aiki.

Labarai Masu Nasaba

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

A lokacin ne na fahimci tabbas ina bukatar daukan wani mataki. A farko-farkon yajin aikin na yi ta kashe kudade saboda ni sabuwa ce a lamarin don haka ban samu damar tara kudade masu yawan da zan iya rike kaina a lokacin yajin aikin ba. Bisa wannan dalilin sai na koma garinmu na asali jihar Filato domin neman mafita.

Na zo na shiga cikin matsalar kudi kai sai da aka zo gabar da ina cin bashi domin na samu yadda zan rike kaina da iyayena.

“Iyayena sun rungumi sana’ar noma hannu biyu-biyu tun ma kafin su yi ritaya a wajen aikinsu, don haka bayan da suka yi ritaya din ma sun cigaba da harkokinsu na noma. A lokacin da na koma gida, na bi su muka shiga harkar noma da tunanin cewa bayan wasu ‘yan makonni za a janye yajin aikin, sai ya zama tunanina na neman zama kamar abun wasa. Na shiga noman tare da iyayena muka share gona, aka yi shuka aka fara girbi har yanzu dai muna gida yajin aiki bai kare ba.

“Kan hakan na fara kokarin tunanin mene ne zan yi da zai ke kawo min kudin shiga ba kuma zan iya tambayar iyayena da suka yi ritaya kudi ba saboda su ma kansu suna fatan samu daga gareni. Daga bisani sai na yanke shawarar cewa na dukufa wajen Saida wasu daga cikin Dankalin da muka noma a gonarmu kuma na san za su yi daraja a Akwa Ibom.

“Da fari na fara saida Dankalin a Jos domin tara kudaden da zan yi jigilar Dankalin Uwa Akwa Ibom. Ta hakan na fara neman yadda zan rike kaina wannan dalilin ne ya sanya na shiga sana’ar saida Dankalin gadan-gadan.”

Da take bayani kan yadda jama’a suke fassara halin da ta shiga, ta ce ko a jikinta domin ita ta san halin da take ciki da kuma yadda za ta rufa wa kanta asiri kuma ta tsira da mutuncinta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUJihar OyoMalamar Jami'aYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Yi Cikakken Bayani Kan Matsayar Sin Game Da Yankin Taiwan

Next Post

Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Related

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

1 hour ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

4 hours ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

5 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

7 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

8 hours ago
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

16 hours ago
Next Post
Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

LABARAI MASU NASABA

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.