ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Malamar Jami'a

Wata Malamar Jami’ar Oyo da ke jihar Akwa Ibom, Misis Christiana Pam, ta ce domin samun abincin da za ta rayu a irin wannan lokacin da kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ke ci gaba da gudanar da yajin aiki, a yanzu haka ta rungumi sana’ar sayar da Dankalin Turawa domin samun abin kai wa baki. 

A ranar 14 ga watan Fabrairu ne kungiyar ASUU ta tsunduma yajin aikin makonni hudu a matsayin gargadi bisa bukatun da suke, daga bisa ta kara tsawaita yajin aikin zuwa wasu watanni biyu a ranar 14 ga watan Maris. Sannan ta sake sanar da wasu karin makonni 12 a ranar 9 ga watan Mayu.

  • Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo
  • Wasu Gwamnatocin Kasashe Sun Nanata Matsayinsu Na Tsaiwa Tsayin Daka Kan Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Yajin aikin kamar yadda kungiyar ta ce, ta shiga ne sakamakon kasa ciki mata alkawuran da suka yi da Gwamnatin tarayya dangane da wasu tilin bukatun da take da su.

ADVERTISEMENT

A hirarta da majiyarmu bayan da hotunan ta suka karade kafafen sadarwar zamani da ke nunata tana sana’ar, Pam ta ce, ta shiga halin matsatsi na rashin kudi sakamakon ita sabuwar ma’aikaciya ce wacce ba ta samu damar tara kudade masu yawan da za ta iya rayuwa muddin yajin aikin ya jima ba.

“Lokacin da aka ayyana yajin aikin wata guda, na yi tsammanin cewa ba za a wuce wannan lokacin ba za a dawo. Na dauka cewa kungiyar ASUU da gwamantin za su samu fahimtar juna kan bukatun ASUU, kwatsam sai kuma hakan ba ta faru ba, a takaice dai aka tsawaita yajin aiki.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

A lokacin ne na fahimci tabbas ina bukatar daukan wani mataki. A farko-farkon yajin aikin na yi ta kashe kudade saboda ni sabuwa ce a lamarin don haka ban samu damar tara kudade masu yawan da zan iya rike kaina a lokacin yajin aikin ba. Bisa wannan dalilin sai na koma garinmu na asali jihar Filato domin neman mafita.

Na zo na shiga cikin matsalar kudi kai sai da aka zo gabar da ina cin bashi domin na samu yadda zan rike kaina da iyayena.

“Iyayena sun rungumi sana’ar noma hannu biyu-biyu tun ma kafin su yi ritaya a wajen aikinsu, don haka bayan da suka yi ritaya din ma sun cigaba da harkokinsu na noma. A lokacin da na koma gida, na bi su muka shiga harkar noma da tunanin cewa bayan wasu ‘yan makonni za a janye yajin aikin, sai ya zama tunanina na neman zama kamar abun wasa. Na shiga noman tare da iyayena muka share gona, aka yi shuka aka fara girbi har yanzu dai muna gida yajin aiki bai kare ba.

“Kan hakan na fara kokarin tunanin mene ne zan yi da zai ke kawo min kudin shiga ba kuma zan iya tambayar iyayena da suka yi ritaya kudi ba saboda su ma kansu suna fatan samu daga gareni. Daga bisani sai na yanke shawarar cewa na dukufa wajen Saida wasu daga cikin Dankalin da muka noma a gonarmu kuma na san za su yi daraja a Akwa Ibom.

“Da fari na fara saida Dankalin a Jos domin tara kudaden da zan yi jigilar Dankalin Uwa Akwa Ibom. Ta hakan na fara neman yadda zan rike kaina wannan dalilin ne ya sanya na shiga sana’ar saida Dankalin gadan-gadan.”

Da take bayani kan yadda jama’a suke fassara halin da ta shiga, ta ce ko a jikinta domin ita ta san halin da take ciki da kuma yadda za ta rufa wa kanta asiri kuma ta tsira da mutuncinta.

Malamar Jami'a
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

Amurka Ce Ke Yi Wa Zaman Lafiya A Zirin Taiwan Barazana

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.