• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Rantse Da Allah Binani Ce Ta Lashe Zaɓen Gwamnan Adamawa A 2023 – Tsohon Kwamishinan Zaɓe

Da Gangan Aka Yi Watsi Da Shaiduna

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
Na Rantse Da Allah Binani Ce Ta Lashe Zaɓen Gwamnan Adamawa A 2023 – Tsohon Kwamishinan Zaɓe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakataccen Kwamishinan zaɓe na jihar Adamawa (REC), Barista Hudu Ari, ya jaddada matsayarsa kan iƙirarin cewa, Sanata Aisha Binani ta jam’iyyar APC ce ta lashe zaɓen gwamnan jihar Adamawa a zaɓen da aka gudanar a shekarar 2023.

 

Ari wanda ya rantse da Al-Ƙur’ani yayin da ke kare matsayarsa, ya haƙiƙance kan cewa, shelanta Binani da ya yi a matsayin wacce ta lashe zaɓen ya yi bisa gaskiya da kwararan hujjoji.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Wani Ɗalibi Da Ya Kashe Abokinshi Da Gatari A Nasarawa 
  • Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a gidansa da ke Bauchi a ranar Asabar, 8 ga watan Fabrairu, Barista Hudu Ari ya ce, ya samu shaidun da suke tabbatar da cewa, Binani ta kayar da gwamna mai ci, Ahmadu Umaru Fintiri na jam’iyyar PDP a yayin zaɓen.

 

Labarai Masu Nasaba

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, an tabbatar da sallamar Ari a matsayin Kwamishinan zaɓen jihar Adamawa bayan da Majalisar wakilai ta tarayya ta amince da buƙatar sallamarsa da shugaban ƙasa ya yi, biyo bayan zarginsa da aka yi da karya ƙa’idojin aiki da shigo da shakku yayin gudanar da aikin zaɓe da ayyana sakamakon zaɓe ba daidai ba, lamarin da har ya kai an gurfanar da shi a kotu.

 

Ari ya nuna damuwarsa kan yadda hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) da kotun sauraron ƙararrakin zaɓe suka shafa wa idanunsu toka suka ƙi hango hujjojinsa da ya gabatar na kura-kuran da aka tafka a lokacin zaɓen.

 

Hudu wanda ya ɗauki Alkur’ani mai girma yayin hirar, ya rantse da Allah cewa, matakin da ya ɗauka a yayin ayyana sakamakon zaɓen ya yi ne da zuciya ɗaya kan gaskiya da kuma bisa dokokin gudanar da zaɓe.

 

Ari ya kuma ce INEC da kotun sauraron ƙararrakin zaɓe ba su ba shi damar kare kansa da ji daga gareshi ba, kuma shaidunsa da suke nuna cewa, Binani ce ta yi nasara an yi watsi da su ba tare da zurfin tunani ko nazarta ba.

 

Ya ce, hatta korarsa da shugaban ƙasa ya yi an yi ne kawai domin ɓata masa kima da mutunci.

 

Kan zargin da aka masa na cewa ya karɓi cin hancin biliyan 2 a wajen ‘yan siyasa domin kare ko yin abun da zai zama alfanu ga Binani, Ari ya ƙaryata. Ya sanar da cewa yanzu haka yana tuntuɓar iyalansa kan ko zai nemi haƙƙi a kotu kan zargi marar tushe da aka masa na amsar na goro, tare da cewa, “Nijeriya ƙasarmu ce dukka, ya rage namu mu kare ƙasar ko mu lalata ta.”

 

Da ya ke bayani kan zamansa a ofis, ya ce, ya samu nasarar gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisu ba tare da wani ce-ce-ku-ce ba.

 

Ya yi iƙirarin cewa batutuwan da suka taso lokacin zaɓen gwamnan jihar da ‘yan majalisun jiha a rumfunan zaɓe 69 su ne suka janyo rikici da har ya kai ga korarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Wani Ɗalibi Da Ya Kashe Abokinshi Da Gatari A Nasarawa 

Next Post

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

Related

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

43 minutes ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

9 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

12 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

13 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

14 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

16 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

'Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.