• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Rantse Da Allah Binani Ce Ta Lashe Zaɓen Gwamnan Adamawa A 2023 – Tsohon Kwamishinan Zaɓe

Da Gangan Aka Yi Watsi Da Shaiduna

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
9 months ago
Binani

Dakataccen Kwamishinan zaɓe na jihar Adamawa (REC), Barista Hudu Ari, ya jaddada matsayarsa kan iƙirarin cewa, Sanata Aisha Binani ta jam’iyyar APC ce ta lashe zaɓen gwamnan jihar Adamawa a zaɓen da aka gudanar a shekarar 2023.

 

Ari wanda ya rantse da Al-Ƙur’ani yayin da ke kare matsayarsa, ya haƙiƙance kan cewa, shelanta Binani da ya yi a matsayin wacce ta lashe zaɓen ya yi bisa gaskiya da kwararan hujjoji.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Wani Ɗalibi Da Ya Kashe Abokinshi Da Gatari A Nasarawa 
  • Me Dakatarwar Da Pillars Ta Yi Wa Usman Abdalla Ke Nufi?

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a gidansa da ke Bauchi a ranar Asabar, 8 ga watan Fabrairu, Barista Hudu Ari ya ce, ya samu shaidun da suke tabbatar da cewa, Binani ta kayar da gwamna mai ci, Ahmadu Umaru Fintiri na jam’iyyar PDP a yayin zaɓen.

 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, an tabbatar da sallamar Ari a matsayin Kwamishinan zaɓen jihar Adamawa bayan da Majalisar wakilai ta tarayya ta amince da buƙatar sallamarsa da shugaban ƙasa ya yi, biyo bayan zarginsa da aka yi da karya ƙa’idojin aiki da shigo da shakku yayin gudanar da aikin zaɓe da ayyana sakamakon zaɓe ba daidai ba, lamarin da har ya kai an gurfanar da shi a kotu.

 

Ari ya nuna damuwarsa kan yadda hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) da kotun sauraron ƙararrakin zaɓe suka shafa wa idanunsu toka suka ƙi hango hujjojinsa da ya gabatar na kura-kuran da aka tafka a lokacin zaɓen.

 

Hudu wanda ya ɗauki Alkur’ani mai girma yayin hirar, ya rantse da Allah cewa, matakin da ya ɗauka a yayin ayyana sakamakon zaɓen ya yi ne da zuciya ɗaya kan gaskiya da kuma bisa dokokin gudanar da zaɓe.

 

Ari ya kuma ce INEC da kotun sauraron ƙararrakin zaɓe ba su ba shi damar kare kansa da ji daga gareshi ba, kuma shaidunsa da suke nuna cewa, Binani ce ta yi nasara an yi watsi da su ba tare da zurfin tunani ko nazarta ba.

 

Ya ce, hatta korarsa da shugaban ƙasa ya yi an yi ne kawai domin ɓata masa kima da mutunci.

 

Kan zargin da aka masa na cewa ya karɓi cin hancin biliyan 2 a wajen ‘yan siyasa domin kare ko yin abun da zai zama alfanu ga Binani, Ari ya ƙaryata. Ya sanar da cewa yanzu haka yana tuntuɓar iyalansa kan ko zai nemi haƙƙi a kotu kan zargi marar tushe da aka masa na amsar na goro, tare da cewa, “Nijeriya ƙasarmu ce dukka, ya rage namu mu kare ƙasar ko mu lalata ta.”

 

Da ya ke bayani kan zamansa a ofis, ya ce, ya samu nasarar gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisu ba tare da wani ce-ce-ku-ce ba.

 

Ya yi iƙirarin cewa batutuwan da suka taso lokacin zaɓen gwamnan jihar da ‘yan majalisun jiha a rumfunan zaɓe 69 su ne suka janyo rikici da har ya kai ga korarsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Labarai

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

'Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

LABARAI MASU NASABA

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

October 23, 2025
Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.