• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata – Gwamnan Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada tabbacin hada hannu da malaman addini domin magance kalubalen talauci da ake fuskanta na sama da kashi 80 cikin 100 a yankunan karkara, za kuma ta mayar da yaran da basu zuwa makaranta ajujuwa domin samun zaman lafiya da cigaba a fadin jihar.

Gwamnan jihar, Malam Uba Sani ne ya bayyana hakan a yayin wani taro da kwamitin addini na jihar Kaduna, domin inganta zaman lafiya da inganta tsaro da aka gudanar a Kaduna.

  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Kaduna Ta Ware Naira Biliyan 3.1 Don Biyan Kuɗin Giratuti

Gwamna Sani ya roki malaman addinin Musulunci da na Kirista da su tallafawa gwamnati ta hanyar wa’azin wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiyansu.

Ya ce, ba za a iya samun zaman lafiya da tsaro a jihar ba, matukar kashi 80 cikin 100 na ‘yan jihar, musamman a yankunan karkara na fama da matsanancin talauci.

A cewarsa, akwai yara sama da 600,000 da ba sa zuwa makaranta a jihar, don haka, ya zama dole ne a mayar da su makaranta domin samun zaman lafiya a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

“Muna fuskantar matsaloli na fama da matsanancin talauci musamman a yankunan karkara. Kashi 80 cikin 100 na mutanen karkara na fama da matsanancin talauci. Wannan shi ne Gaskiyar magana.

“A watan da ya gabata, mun fara aikin gina tituna 32 a fadin jihar, wadanda akasarinsu na yankunan karkara ne.”

Gwamna Uba Sani ya kuma bayyana cewa, daga mako mai zuwa, gwamnatin jihar Kaduna za ta fara gina makarantu 100 domin mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta ajujuwa domin magance matsalar rashin zuwa makaranta.

“An bar yara ba sa zuwa makaranta, suna yawo a kan tituna kuma a ce ana son a magance matsalar rashin tsaro? Ba zai yi wu ba. Don haka, dole ne a mayar da su makaranta.

“Bincikenmu ya nuna cewa, saboda talauci ne yawancin yaran ba su zuwa makaranta. Mutanen karkara ba sa tura ‘ya’yansu makaranta domin suna son su je gona ko kuma su tafi talla. Don haka, idan ba mu rage talauci daga kashi 80 cikin 100 zuwa akalla kashi 30 cikin 100 nan da shekaru masu zuwa ba, ba za mu taba iya magance matsalar yaran da ba su zuwa makaranta.”

Gwamnan ya jaddada cewa, dole ne gwamnatin ta farfado da tattalin arzikin yankunan karkara ta hanyar samar da ayyukan yi domin kawo karshen talauci.

Malam Uba Sani ya kuma bayyana cewa, gwamnatin Kaduna za ta hada kai da malaman addini wajen samar da bayanan marayu 5,000 a jihar domin basu tallafin karatu da gidauniyar tallafi ta Qatar ke daukar nauyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KadunaKalubalen rashin zuwa makarantaTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

Next Post

Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

2 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

4 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

4 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

8 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

10 hours ago
Next Post
dala

Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.