• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata – Gwamnan Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada tabbacin hada hannu da malaman addini domin magance kalubalen talauci da ake fuskanta na sama da kashi 80 cikin 100 a yankunan karkara, za kuma ta mayar da yaran da basu zuwa makaranta ajujuwa domin samun zaman lafiya da cigaba a fadin jihar.

Gwamnan jihar, Malam Uba Sani ne ya bayyana hakan a yayin wani taro da kwamitin addini na jihar Kaduna, domin inganta zaman lafiya da inganta tsaro da aka gudanar a Kaduna.

  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Kaduna Ta Ware Naira Biliyan 3.1 Don Biyan Kuɗin Giratuti

Gwamna Sani ya roki malaman addinin Musulunci da na Kirista da su tallafawa gwamnati ta hanyar wa’azin wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiyansu.

Ya ce, ba za a iya samun zaman lafiya da tsaro a jihar ba, matukar kashi 80 cikin 100 na ‘yan jihar, musamman a yankunan karkara na fama da matsanancin talauci.

A cewarsa, akwai yara sama da 600,000 da ba sa zuwa makaranta a jihar, don haka, ya zama dole ne a mayar da su makaranta domin samun zaman lafiya a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

“Muna fuskantar matsaloli na fama da matsanancin talauci musamman a yankunan karkara. Kashi 80 cikin 100 na mutanen karkara na fama da matsanancin talauci. Wannan shi ne Gaskiyar magana.

“A watan da ya gabata, mun fara aikin gina tituna 32 a fadin jihar, wadanda akasarinsu na yankunan karkara ne.”

Gwamna Uba Sani ya kuma bayyana cewa, daga mako mai zuwa, gwamnatin jihar Kaduna za ta fara gina makarantu 100 domin mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta ajujuwa domin magance matsalar rashin zuwa makaranta.

“An bar yara ba sa zuwa makaranta, suna yawo a kan tituna kuma a ce ana son a magance matsalar rashin tsaro? Ba zai yi wu ba. Don haka, dole ne a mayar da su makaranta.

“Bincikenmu ya nuna cewa, saboda talauci ne yawancin yaran ba su zuwa makaranta. Mutanen karkara ba sa tura ‘ya’yansu makaranta domin suna son su je gona ko kuma su tafi talla. Don haka, idan ba mu rage talauci daga kashi 80 cikin 100 zuwa akalla kashi 30 cikin 100 nan da shekaru masu zuwa ba, ba za mu taba iya magance matsalar yaran da ba su zuwa makaranta.”

Gwamnan ya jaddada cewa, dole ne gwamnatin ta farfado da tattalin arzikin yankunan karkara ta hanyar samar da ayyukan yi domin kawo karshen talauci.

Malam Uba Sani ya kuma bayyana cewa, gwamnatin Kaduna za ta hada kai da malaman addini wajen samar da bayanan marayu 5,000 a jihar domin basu tallafin karatu da gidauniyar tallafi ta Qatar ke daukar nauyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KadunaKalubalen rashin zuwa makarantaTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

Next Post

Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli

Related

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

8 minutes ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

5 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

7 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

8 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

10 hours ago
Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni
Labarai

Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

12 hours ago
Next Post
dala

Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

August 1, 2025
Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

August 1, 2025
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

August 1, 2025
Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati

August 1, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 01-07-2025

August 1, 2025
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.