ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata – Gwamnan Kaduna

by Sulaiman
3 years ago
Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada tabbacin hada hannu da malaman addini domin magance kalubalen talauci da ake fuskanta na sama da kashi 80 cikin 100 a yankunan karkara, za kuma ta mayar da yaran da basu zuwa makaranta ajujuwa domin samun zaman lafiya da cigaba a fadin jihar.

Gwamnan jihar, Malam Uba Sani ne ya bayyana hakan a yayin wani taro da kwamitin addini na jihar Kaduna, domin inganta zaman lafiya da inganta tsaro da aka gudanar a Kaduna.

  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai
  • Gwamnatin Kaduna Ta Ware Naira Biliyan 3.1 Don Biyan Kuɗin Giratuti

Gwamna Sani ya roki malaman addinin Musulunci da na Kirista da su tallafawa gwamnati ta hanyar wa’azin wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiyansu.

ADVERTISEMENT

Ya ce, ba za a iya samun zaman lafiya da tsaro a jihar ba, matukar kashi 80 cikin 100 na ‘yan jihar, musamman a yankunan karkara na fama da matsanancin talauci.

A cewarsa, akwai yara sama da 600,000 da ba sa zuwa makaranta a jihar, don haka, ya zama dole ne a mayar da su makaranta domin samun zaman lafiya a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Muna fuskantar matsaloli na fama da matsanancin talauci musamman a yankunan karkara. Kashi 80 cikin 100 na mutanen karkara na fama da matsanancin talauci. Wannan shi ne Gaskiyar magana.

“A watan da ya gabata, mun fara aikin gina tituna 32 a fadin jihar, wadanda akasarinsu na yankunan karkara ne.”

Gwamna Uba Sani ya kuma bayyana cewa, daga mako mai zuwa, gwamnatin jihar Kaduna za ta fara gina makarantu 100 domin mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta ajujuwa domin magance matsalar rashin zuwa makaranta.

“An bar yara ba sa zuwa makaranta, suna yawo a kan tituna kuma a ce ana son a magance matsalar rashin tsaro? Ba zai yi wu ba. Don haka, dole ne a mayar da su makaranta.

“Bincikenmu ya nuna cewa, saboda talauci ne yawancin yaran ba su zuwa makaranta. Mutanen karkara ba sa tura ‘ya’yansu makaranta domin suna son su je gona ko kuma su tafi talla. Don haka, idan ba mu rage talauci daga kashi 80 cikin 100 zuwa akalla kashi 30 cikin 100 nan da shekaru masu zuwa ba, ba za mu taba iya magance matsalar yaran da ba su zuwa makaranta.”

Gwamnan ya jaddada cewa, dole ne gwamnatin ta farfado da tattalin arzikin yankunan karkara ta hanyar samar da ayyukan yi domin kawo karshen talauci.

Malam Uba Sani ya kuma bayyana cewa, gwamnatin Kaduna za ta hada kai da malaman addini wajen samar da bayanan marayu 5,000 a jihar domin basu tallafin karatu da gidauniyar tallafi ta Qatar ke daukar nauyi.

Kaduna
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
dala

Dage Takunkumin Canjin Dala Ga Masu Shigo Da Kaya 43 A Sikeli

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.