• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Sha Duka Kafin A Amince In Shiga Harkar Fim – Khadija Mai Numfashi

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Khadija Mai Numfashi

Jarumar Kannywood Khadija Ahmed wadda akafi sani da Khadija Mai Numfashi a wata hira da ta yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna Gabon’s Room Talk Show ta bayyana yadda ta sha gwagwarmaya a lokacin da ta nuna sha’awar fara fitowa a cikin shirin fina-finan Hausa na Kannywood.

Jarumar wadda hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano (Kano State Censorship Board) ta dakatar daga shiga duk wata harka ta shirin fim na tsawon lokaci sakamakon wani faifan bidiyo nata da ta dora a kan shafinta na Tik Tok ta bayyana cewar ta sha wahala kafin a amince mata ta shiga masana’antar Kannywood a wancan lokacin.

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Fati Slow Ta Rasu
  • Rahama Sadau: Daga Jarumar Kannywood Ta Zama Jarumar Bollywood

A lokacin da na bukaci shiga harkar fim sai na tuntubi Ayatullahi wanda a wancan lokacin yake kamar saurayina, sai ya nuna mani cewar ba za a fara haskani a cikin shirin fim ba sai da umarnin iyayena, ni kuma da yake ina matukar sha’awar fitowa a cikin shirin fim a wancan lokacin sai nace masa an amince in fara fim a gidanmu, in ji Mai Numfashi.

Ta ci gaba da cewa bayan na fito a wani fim ne sai kanin mahaifiyata ya kira ni, a lokacin da ya nuna mani bidiyon sai yake tambayata nan wacece kafin in bashi amsa tuni ya falla mani mari a kumatu ni kuma na fashe da kuka.

Haka dai na ci gaba da ganin kalubale kala kala inda gaba daya ‘yan uwan mahaifiyata suka ki amincewa in yi fim har sai lokacin da aka tafi dani da mahaifiyata har inda ake daukar wani shiri, bayan taga yadda ake yi sai ta ce mani indai har iyakar abinda ake yi kenan a fim to ina yi maki fatan alheri Allah ya bada sa a.

LABARAI MASU NASABA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Da aka tambayeta a kan ko ta yi nadamar abinda ta aikata har yaka ga hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano a karkashin jagorancin Abba El Mustapha ta dakatar da ita daga shiga duk wata harka ta fim na tsawon wani lokaci.

Sai Khadija ta ce maganar nadama kam sosai ta yi nadamar abinda ta aikata har ya kai ga an dakatar da ita, inda kuma ta ce a halin yanzu ta yi wa kanta fada domin ganin cewar hakan bata sake faruwa anan gaba ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Next Post
Kasar Sin Ba Za Ta Jure Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidanta Da Wasu Kasashen Waje Ke Yi Kan Batun Taiwan Ba

Kasar Sin Ba Za Ta Jure Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidanta Da Wasu Kasashen Waje Ke Yi Kan Batun Taiwan Ba

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.