• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

by Muhammad
4 months ago
Soja

Marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa dalilin da ya sa ya shiga rundunar sojin Nijeriya, shi ne domin gujewa auren fari da wuri da aka so yi masa a ƙuruciyarsa a garinsu na Daura, Jihar Katsina a yau.

Buhari ya bayyana hakan ne a lokacin da yake hira da tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Farfesa Isa Ali Pantami, a gidansa da ke Daura, bayan barinsa mulki a shekarar 2023.

  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
  • Rasuwar Buhari: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Yau Litinin A Matsayin Ranar Hutun Aiki A Jihar

Bidiyon hirar, wanda ya sake bayyana a kafafen sada zumunta bayan rasuwarsa, ya nuna Buhari cikin walwala yana ba da labarin rayuwarsa bayan kammala karatun sakandare.

Pantami ya tunatar da Buhari kan irin nasarorin da ya samu a aikin soja, musamman a Gombe tsakanin 1984 da 1985.

A martaninsa kan dalilin shiga soji, Buhari ya ce: “Na shiga soja ne domin gujewa aure da wuri da aka shirya yi min.”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Ya ƙara da cewa: “Bayan shekaru tara da na yi ina karatu a Katsina, shekara uku a makarantar firamare ta gaba da sakandare shekaru shida, na dawo gida, sai suka shirya yi mini aure. Wata rana na ci karo da wani da ban san shi ba wanda daga baya aka ce ɗan uwan mahaifina ne. Ya buƙaci na kai shi wurin mahaifiyata, kuma daga baya aka ce an ba ni diyarsa ta aureni, ko yana raye, ko bayan ba ransa ya ba ni ɗiyarsa halin.”

Ya ce, a lokacin da ya gama karatu, an yi masa tayin aiki da albashin fam £12.10 da babur da kuma mata damar zama a wurin na har abada.

“A lokacin ne na yanke shawarar na gudu, na shiga aikin soja,” in ji shi cikin dariya. “Mahaifiyata ta damu ƙwarai saboda haka, na ci gaba da bata hakuri har tsawon lokaci. Ta ce tana so ta ga zuriyar ɗanta na ƙarshe. Haka na samu kaina a cikin soji.”

Marigayi Buhari, wanda ya mulki Nijeriya a matsayin shugaban mulkin soja daga 1983 zuwa 1985, sannan kuma ya sake zama shugaban ƙasa a mulkin dimokuraɗiyya daga 2015 zuwa 2023, ya rasu a asibiti da ke Lolandon yana da shekara 82, bayan fama da rashin lafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Next Post
Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.