• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

by Muhammad
3 hours ago
in Labarai, Rahotonni
0
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa dalilin da ya sa ya shiga rundunar sojin Nijeriya, shi ne domin gujewa auren fari da wuri da aka so yi masa a ƙuruciyarsa a garinsu na Daura, Jihar Katsina a yau.

Buhari ya bayyana hakan ne a lokacin da yake hira da tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Farfesa Isa Ali Pantami, a gidansa da ke Daura, bayan barinsa mulki a shekarar 2023.

  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
  • Rasuwar Buhari: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Yau Litinin A Matsayin Ranar Hutun Aiki A Jihar

Bidiyon hirar, wanda ya sake bayyana a kafafen sada zumunta bayan rasuwarsa, ya nuna Buhari cikin walwala yana ba da labarin rayuwarsa bayan kammala karatun sakandare.

Pantami ya tunatar da Buhari kan irin nasarorin da ya samu a aikin soja, musamman a Gombe tsakanin 1984 da 1985.

A martaninsa kan dalilin shiga soji, Buhari ya ce: “Na shiga soja ne domin gujewa aure da wuri da aka shirya yi min.”

Labarai Masu Nasaba

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

Ya ƙara da cewa: “Bayan shekaru tara da na yi ina karatu a Katsina, shekara uku a makarantar firamare ta gaba da sakandare shekaru shida, na dawo gida, sai suka shirya yi mini aure. Wata rana na ci karo da wani da ban san shi ba wanda daga baya aka ce ɗan uwan mahaifina ne. Ya buƙaci na kai shi wurin mahaifiyata, kuma daga baya aka ce an ba ni diyarsa ta aureni, ko yana raye, ko bayan ba ransa ya ba ni ɗiyarsa halin.”

Ya ce, a lokacin da ya gama karatu, an yi masa tayin aiki da albashin fam £12.10 da babur da kuma mata damar zama a wurin na har abada.

“A lokacin ne na yanke shawarar na gudu, na shiga aikin soja,” in ji shi cikin dariya. “Mahaifiyata ta damu ƙwarai saboda haka, na ci gaba da bata hakuri har tsawon lokaci. Ta ce tana so ta ga zuriyar ɗanta na ƙarshe. Haka na samu kaina a cikin soji.”

Marigayi Buhari, wanda ya mulki Nijeriya a matsayin shugaban mulkin soja daga 1983 zuwa 1985, sannan kuma ya sake zama shugaban ƙasa a mulkin dimokuraɗiyya daga 2015 zuwa 2023, ya rasu a asibiti da ke Lolandon yana da shekara 82, bayan fama da rashin lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AureBuhariDauraGwamnatin KatsinaKatsinaRasuwar BuhariSoja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari

Next Post

Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

Related

Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi
Manyan Labarai

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

8 minutes ago
Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida
Manyan Labarai

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

35 minutes ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

52 minutes ago
Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari
Labarai

Sarkin Musulmi, Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari

1 hour ago
Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari
Labarai

Mutuwar Buhari Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Kashim Shettima

2 hours ago
Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

2 hours ago
Next Post
Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

July 14, 2025
Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

July 14, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

July 14, 2025
Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

Sarkin Musulmi, Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

Mutuwar Buhari Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Kashim Shettima

July 14, 2025
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi

Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi

July 14, 2025
Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

July 14, 2025
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

July 14, 2025
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Rasuwar Buhari: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Yau Litinin A Matsayin Ranar Hutun Aiki A Jihar

Rasuwar Buhari: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Yau Litinin A Matsayin Ranar Hutun Aiki A Jihar

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.