Sojojin Nijeriya sun cafke ƴan ta’adda 20, sun kuma ceto mutane 17 da aka yi garkuwa da su a jerin hare-hare da binciken leƙen asiri da suka gudanar a sassa daban-daban. Haka kuma, sun gano wuraren tace haramtaccen Mai a yankin Kudu maso Kudu.
Wata majiyar daga shalƙwatar rundunar Sojin ta bayyana cewa ƴan ta’adda uku — Fannami Ari (Abu Dujana), da Hussaini Hassan Modu (Abu Yusuf) da wani mai koyon ta’addanci — sun miƙa wuya ga Sojoji a ƙananan hukumomin Kukawa da Damboa na Jihar Borno, bayan sun gaji da zaluncin shugabanninsu da tsananin rayuwa a sansanoninsu.
- Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno
A yankin Arewa maso Gabas, Sojojin bataliya ta 192 tare da CJTF sun yi artabu da mayaƙan ISWAP da Boko Haram (JAS) a ƙauyen Hudugum na ƙaramar hukumar Gwoza, inda suka kashe ƴan ta’adda biyu. A Arewa maso Yamma kuwa, Sojojin Birgediya ta 1 sun daƙile sace mutane a Zamfara, inda suka ceto mutane 11 a yankunan Magami–Jan Gemi da Kucheri–Bilbis.
A Arewa ta Tsakiya, Sojojin Operation Enduring Peace (OPEP) da Operation Whirl Stroke (OPWS) sun gudanar da hare-hare a jihohin Filato, da Benue, da Nasarawa da Kaduna, inda suka kama mutane 15 da ake zargi da laifukan ta’addanci, da satar shanu da rikice-rikicen ƙabilanci, tare da ceto mutane 4 da aka yi garkuwa da su a Filato da Taraba.
Haka kuma, a Kudu maso Kudu, Sojojin Bataliya ta 29 sun lalata karatun tace haramtaccen Mai guda biyu a yankin Biseni na Jihar Bayelsa, yayin da Birgediya ta 34 ta kama ganguna 62 na man fetur da aka sace — kimanin lita 3,000 a Ohaji/Egbema na Jihar Imo, domin daƙile aiyukan masu satar mai.














