• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Kafa Kwamitin Karbar Korafe-korafe

by Sulaiman and Bello Hamza
10 months ago
in Labarai
0
Nahcon
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Domin kara inganta ayyyukan ta, Hukumar Aikin Hajji ta Nijeriya NAHCON ta kafa kwamiti domin karbar korafa-korarfe daga wadanda suka yi aikin Hajjin bana da kuma wadanda suka gudanar da aiki Umara kuma suna da wani korafi a kan hukumar ko kuma wani ma’aikaci ko kuma bangaren masu ayyuka a karkashin hukumar, dasu gabatar da korafinsu ga hukumar domin daukar matakin gyara a yayin aikin hajjin shekara mai zuwa.

Bayanin haka ya fito ne a takardar sanarwa da hukumar ta buga a wasu jaridun kasar nan, hakan kuma ya biyo bayan wasu korafe-korafe ne wasu masu ruwa da tsaki suka gabatar a kafafen sadarwa na intanet ciki har da Gwmanan Jihar Neja Muhammad Bago, inda ya nemi a rusa hukumar a dawo da harkokin aikin hajji ga jihohi.

  • Zai Yi Wahala A Magance Matsalar Tsaro Matukar… – Janar Lagbaja
  • Peng Liyuan Ta Yi Kira Da Karin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasa Da Kasa Domin Takaita Cututtukan Kanjamau Da Tarin Fuka

Sanarwa ta bayar da wa’adin zuwa ranar 10 ga watan Agusta 2024 ga duk duk wanda yake da wani tsokaci ko shawarwari na yadda za a kara inganta aikin Hajji da Umara a shekara mai zuwa ya gabatar wa hukumar.

An kuma bukaci duk mai korafi ya rubuta cikakken sunansa da adireshinsa ya kuma aika zuwa hedikwatar hukumar da ke Abuja.

A wani bangaren kuma Hukumar Koli ta Addinin Musulunci (NSCIA) ta bayyana aniyyarta na bincikar Hukumar Aikin ta Nijeriya NAHCON a kan yadda ta gudanar da aikin hajjin bana musamman ganin yadda aka samu korarfe-korafe daga bangarori da dama, musamman daga masu ruwa da tsaki inda suka nuna rasahin gamsuwarsu a kan yadda aka gudanar da wasu lamurrori da suka shafi aikin hajjin bana.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar ta bayyana wannan shiri nata ne bayan taron da ta gabatar na kwamitin zartarwarta da aka yi a babban dakin taron babban masallacin kasa da ke Abuja ranar Asabar 6 ga watan Yuli 2024.

A takaradar bayan taron da babban sakatarenta, Farfesa Isahak Oloyede ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa, a halin yanzu hukumar na jiran rahoton yadda aka gudanar da aikin hajjin ne daga NAHCON kafin ta fara gudanar da nata binciken da bin diddigin korarfe-korafen da masu ryuwa da tsaki suka gabatar a kan yadda aka gudanar da aikin hajjin bana.

Hukumar wadda ita ce, a kan gaba a cikin kungiyoyin addinin musulunci a Nijeriya ta kara da cewa, “Ganin korafe-korafe daga masu ruwa  da tsaki a kan yadda aka gudanar da harkokin da suka shafi aikin hajjin bana, taron ya yanke shawarar a jira fitiowar rahoton NAHCON a kan yadda ta jagoranci aikin hajin bana kafin a fara aikin binciken, an kuma amince da kiran babban taro na kasa domin tattauna lamarin aikin hajjin gaba daya. An kuma nuna bukatar a samar da hanyar tattaunawa a tsakanin gwanmati, NAHCON da kuma kungiyar NSCIA domin samun fahimtar juna a dukkan matakan aikin hajji, ta haka ne al’ummar musulmi musamman alhazai za su amfana da irin gudummawar da gwamnati ke bayarwa a duk shekara a kan aikin hajji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hajjin BanaNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Samu Sakamako Mai Kyau A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Next Post

Ƴan Jarida Biyu da Aka Sace a Kaduna Sun Shaƙi Iskar Ƴanci

Related

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

42 minutes ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

2 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

3 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

4 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

5 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

6 hours ago
Next Post
Ƴan Jarida Biyu da Aka Sace a Kaduna Sun Shaƙi Iskar Ƴanci

Ƴan Jarida Biyu da Aka Sace a Kaduna Sun Shaƙi Iskar Ƴanci

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.