ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Kafa Kwamitin Karbar Korafe-korafe

by Sulaiman and Bello Hamza
1 year ago
Nahcon

Domin kara inganta ayyyukan ta, Hukumar Aikin Hajji ta Nijeriya NAHCON ta kafa kwamiti domin karbar korafa-korarfe daga wadanda suka yi aikin Hajjin bana da kuma wadanda suka gudanar da aiki Umara kuma suna da wani korafi a kan hukumar ko kuma wani ma’aikaci ko kuma bangaren masu ayyuka a karkashin hukumar, dasu gabatar da korafinsu ga hukumar domin daukar matakin gyara a yayin aikin hajjin shekara mai zuwa.

Bayanin haka ya fito ne a takardar sanarwa da hukumar ta buga a wasu jaridun kasar nan, hakan kuma ya biyo bayan wasu korafe-korafe ne wasu masu ruwa da tsaki suka gabatar a kafafen sadarwa na intanet ciki har da Gwmanan Jihar Neja Muhammad Bago, inda ya nemi a rusa hukumar a dawo da harkokin aikin hajji ga jihohi.

  • Zai Yi Wahala A Magance Matsalar Tsaro Matukar… – Janar Lagbaja
  • Peng Liyuan Ta Yi Kira Da Karin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasa Da Kasa Domin Takaita Cututtukan Kanjamau Da Tarin Fuka

Sanarwa ta bayar da wa’adin zuwa ranar 10 ga watan Agusta 2024 ga duk duk wanda yake da wani tsokaci ko shawarwari na yadda za a kara inganta aikin Hajji da Umara a shekara mai zuwa ya gabatar wa hukumar.

ADVERTISEMENT

An kuma bukaci duk mai korafi ya rubuta cikakken sunansa da adireshinsa ya kuma aika zuwa hedikwatar hukumar da ke Abuja.

A wani bangaren kuma Hukumar Koli ta Addinin Musulunci (NSCIA) ta bayyana aniyyarta na bincikar Hukumar Aikin ta Nijeriya NAHCON a kan yadda ta gudanar da aikin hajjin bana musamman ganin yadda aka samu korarfe-korafe daga bangarori da dama, musamman daga masu ruwa da tsaki inda suka nuna rasahin gamsuwarsu a kan yadda aka gudanar da wasu lamurrori da suka shafi aikin hajjin bana.

LABARAI MASU NASABA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

Hukumar ta bayyana wannan shiri nata ne bayan taron da ta gabatar na kwamitin zartarwarta da aka yi a babban dakin taron babban masallacin kasa da ke Abuja ranar Asabar 6 ga watan Yuli 2024.

A takaradar bayan taron da babban sakatarenta, Farfesa Isahak Oloyede ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa, a halin yanzu hukumar na jiran rahoton yadda aka gudanar da aikin hajjin ne daga NAHCON kafin ta fara gudanar da nata binciken da bin diddigin korarfe-korafen da masu ryuwa da tsaki suka gabatar a kan yadda aka gudanar da aikin hajjin bana.

Hukumar wadda ita ce, a kan gaba a cikin kungiyoyin addinin musulunci a Nijeriya ta kara da cewa, “Ganin korafe-korafe daga masu ruwa  da tsaki a kan yadda aka gudanar da harkokin da suka shafi aikin hajjin bana, taron ya yanke shawarar a jira fitiowar rahoton NAHCON a kan yadda ta jagoranci aikin hajin bana kafin a fara aikin binciken, an kuma amince da kiran babban taro na kasa domin tattauna lamarin aikin hajjin gaba daya. An kuma nuna bukatar a samar da hanyar tattaunawa a tsakanin gwanmati, NAHCON da kuma kungiyar NSCIA domin samun fahimtar juna a dukkan matakan aikin hajji, ta haka ne al’ummar musulmi musamman alhazai za su amfana da irin gudummawar da gwamnati ke bayarwa a duk shekara a kan aikin hajji.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas
Labarai

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
NBS
Labarai

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Next Post
Ƴan Jarida Biyu da Aka Sace a Kaduna Sun Shaƙi Iskar Ƴanci

Ƴan Jarida Biyu da Aka Sace a Kaduna Sun Shaƙi Iskar Ƴanci

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.