ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Kafa Kwamitin Karbar Korafe-korafe

by Sulaiman and Bello Hamza
2 years ago
Nahcon

Domin kara inganta ayyyukan ta, Hukumar Aikin Hajji ta Nijeriya NAHCON ta kafa kwamiti domin karbar korafa-korarfe daga wadanda suka yi aikin Hajjin bana da kuma wadanda suka gudanar da aiki Umara kuma suna da wani korafi a kan hukumar ko kuma wani ma’aikaci ko kuma bangaren masu ayyuka a karkashin hukumar, dasu gabatar da korafinsu ga hukumar domin daukar matakin gyara a yayin aikin hajjin shekara mai zuwa.

Bayanin haka ya fito ne a takardar sanarwa da hukumar ta buga a wasu jaridun kasar nan, hakan kuma ya biyo bayan wasu korafe-korafe ne wasu masu ruwa da tsaki suka gabatar a kafafen sadarwa na intanet ciki har da Gwmanan Jihar Neja Muhammad Bago, inda ya nemi a rusa hukumar a dawo da harkokin aikin hajji ga jihohi.

  • Zai Yi Wahala A Magance Matsalar Tsaro Matukar… – Janar Lagbaja
  • Peng Liyuan Ta Yi Kira Da Karin Hadin Gwiwa Tsakanin Kasa Da Kasa Domin Takaita Cututtukan Kanjamau Da Tarin Fuka

Sanarwa ta bayar da wa’adin zuwa ranar 10 ga watan Agusta 2024 ga duk duk wanda yake da wani tsokaci ko shawarwari na yadda za a kara inganta aikin Hajji da Umara a shekara mai zuwa ya gabatar wa hukumar.

ADVERTISEMENT

An kuma bukaci duk mai korafi ya rubuta cikakken sunansa da adireshinsa ya kuma aika zuwa hedikwatar hukumar da ke Abuja.

A wani bangaren kuma Hukumar Koli ta Addinin Musulunci (NSCIA) ta bayyana aniyyarta na bincikar Hukumar Aikin ta Nijeriya NAHCON a kan yadda ta gudanar da aikin hajjin bana musamman ganin yadda aka samu korarfe-korafe daga bangarori da dama, musamman daga masu ruwa da tsaki inda suka nuna rasahin gamsuwarsu a kan yadda aka gudanar da wasu lamurrori da suka shafi aikin hajjin bana.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

Hukumar ta bayyana wannan shiri nata ne bayan taron da ta gabatar na kwamitin zartarwarta da aka yi a babban dakin taron babban masallacin kasa da ke Abuja ranar Asabar 6 ga watan Yuli 2024.

A takaradar bayan taron da babban sakatarenta, Farfesa Isahak Oloyede ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa, a halin yanzu hukumar na jiran rahoton yadda aka gudanar da aikin hajjin ne daga NAHCON kafin ta fara gudanar da nata binciken da bin diddigin korarfe-korafen da masu ryuwa da tsaki suka gabatar a kan yadda aka gudanar da aikin hajjin bana.

Hukumar wadda ita ce, a kan gaba a cikin kungiyoyin addinin musulunci a Nijeriya ta kara da cewa, “Ganin korafe-korafe daga masu ruwa  da tsaki a kan yadda aka gudanar da harkokin da suka shafi aikin hajjin bana, taron ya yanke shawarar a jira fitiowar rahoton NAHCON a kan yadda ta jagoranci aikin hajin bana kafin a fara aikin binciken, an kuma amince da kiran babban taro na kasa domin tattauna lamarin aikin hajjin gaba daya. An kuma nuna bukatar a samar da hanyar tattaunawa a tsakanin gwanmati, NAHCON da kuma kungiyar NSCIA domin samun fahimtar juna a dukkan matakan aikin hajji, ta haka ne al’ummar musulmi musamman alhazai za su amfana da irin gudummawar da gwamnati ke bayarwa a duk shekara a kan aikin hajji.

Nahcon
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • Sulaiman
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani
Nahcon
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
Labarai

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Labarai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
Next Post
Ƴan Jarida Biyu da Aka Sace a Kaduna Sun Shaƙi Iskar Ƴanci

Ƴan Jarida Biyu da Aka Sace a Kaduna Sun Shaƙi Iskar Ƴanci

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.