• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Za Ta Gina Masana`antar Samar Da Kayan Samar Da Wuta Ta Hanyar Hasken Rana

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Najeriya Za Ta Gina Masana`antar Samar Da Kayan Samar Da Wuta Ta Hanyar Hasken Rana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya juma`a 24 ga watan nan ne mataimakin shugaban tarayyar Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo, ya jagoranci bikin aza harsashin ginin masana`antar samar da kayan sarrafa hasken rana, domin samar da wutar lantarki a jihar Nasarawa dake shiyyar arewa ta tsakiyar Najeriya.

Ita dai wannan masana`anta, wadda za ta lashe tsabar kudi har Dala biliyan 71.19, za ta kasance irin ta ta farko a yammacin Afrika baki daya idan har an kammala ta.

  • An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da aikin a garin Gora dake jihar ta Nasarawa, mataimakin shugaban kasa Farfessa Yemi Osinbajo ya ce kasancewar jihar ta Nasarawa tana da arzikin sinadaran da ake amfani da su wajen samar da falankin dake zuko hasken rana don sarrafawa zuwa wuta ya sanya gwamnatin tarayyar yanke shawarar kaddamar da wannan gagarumin aiki a jihar.

Ya ce matakin zai taimaka sosai wajen aza Najeriya cikin sahun kasashe makwafta da suke amfani da hanyoyin samar da wuta domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli.

Aikin kamar yadda mataimakin shugaban kasar ya fada zai gudana ne karkashin kulawar hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya wato NASENI har ila yau yana daya daga cikin kokarin gwamantin Najeriya wajen tabbatar da ganin ta kara fadada saka jarin ta a fagen samar da makamashi.

Labarai Masu Nasaba

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Kuma akwai kyakkywan fatan aikin zai iya kawo sauyi mai ma`ana ta fuskar sake fasalin wutar latarki da makamashi a Najeriya.

“Wannan masana`anta zata zo a lokacin da ya dace, inda ban da cin gajiyar ta da jama’a zasuyi, ta zo kuma daidai manufa da shirye shiryen kungiyar tarayyar Afrika ta amfani a sabbin hanyoyin samar da makamashi domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli, baya ga tasirin da za ta yi wajen kawo saukin farashin na`urorin samar da wuta ta hasken rana a Najeriya”

A nasa jawabin, shugaban hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya Farfesa Muhammad Haruna cewa yayi tun shekaru goma da suka gabata hukumar ta tsunduma cikin harkar samar da wuta ta amfani da makamashin solar a Najeriya.

“Hukumar NASENI karkashin jagoranci na da kuma gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari sun damu mutuka bisa yanayi wutar lantarki a Najeriya, wannan ce ta sa aka mayar da hankali wajen amfani da kimiya da kirkire-kirkiren fasaha na cikin gida wajen amfani da albarkatun cikin gida domin kawo dauki ga shirin gwamnati na sake fasalta harkokin wuta a kasa” (Garba Abdullahi Bagwai)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Abba Kyari Ta Dakatar Da Bincikensa

Related

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

5 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

6 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

8 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

9 hours ago
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya
Daga Birnin Sin

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

10 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

12 hours ago
Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Abba Kyari Ta Dakatar Da Bincikensa

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.