• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Za Ta Gina Masana`antar Samar Da Kayan Samar Da Wuta Ta Hanyar Hasken Rana

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Najeriya Za Ta Gina Masana`antar Samar Da Kayan Samar Da Wuta Ta Hanyar Hasken Rana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya juma`a 24 ga watan nan ne mataimakin shugaban tarayyar Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo, ya jagoranci bikin aza harsashin ginin masana`antar samar da kayan sarrafa hasken rana, domin samar da wutar lantarki a jihar Nasarawa dake shiyyar arewa ta tsakiyar Najeriya.

Ita dai wannan masana`anta, wadda za ta lashe tsabar kudi har Dala biliyan 71.19, za ta kasance irin ta ta farko a yammacin Afrika baki daya idan har an kammala ta.

  • An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da aikin a garin Gora dake jihar ta Nasarawa, mataimakin shugaban kasa Farfessa Yemi Osinbajo ya ce kasancewar jihar ta Nasarawa tana da arzikin sinadaran da ake amfani da su wajen samar da falankin dake zuko hasken rana don sarrafawa zuwa wuta ya sanya gwamnatin tarayyar yanke shawarar kaddamar da wannan gagarumin aiki a jihar.

Ya ce matakin zai taimaka sosai wajen aza Najeriya cikin sahun kasashe makwafta da suke amfani da hanyoyin samar da wuta domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli.

Aikin kamar yadda mataimakin shugaban kasar ya fada zai gudana ne karkashin kulawar hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya wato NASENI har ila yau yana daya daga cikin kokarin gwamantin Najeriya wajen tabbatar da ganin ta kara fadada saka jarin ta a fagen samar da makamashi.

Labarai Masu Nasaba

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Kuma akwai kyakkywan fatan aikin zai iya kawo sauyi mai ma`ana ta fuskar sake fasalin wutar latarki da makamashi a Najeriya.

“Wannan masana`anta zata zo a lokacin da ya dace, inda ban da cin gajiyar ta da jama’a zasuyi, ta zo kuma daidai manufa da shirye shiryen kungiyar tarayyar Afrika ta amfani a sabbin hanyoyin samar da makamashi domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli, baya ga tasirin da za ta yi wajen kawo saukin farashin na`urorin samar da wuta ta hasken rana a Najeriya”

A nasa jawabin, shugaban hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya Farfesa Muhammad Haruna cewa yayi tun shekaru goma da suka gabata hukumar ta tsunduma cikin harkar samar da wuta ta amfani da makamashin solar a Najeriya.

“Hukumar NASENI karkashin jagoranci na da kuma gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari sun damu mutuka bisa yanayi wutar lantarki a Najeriya, wannan ce ta sa aka mayar da hankali wajen amfani da kimiya da kirkire-kirkiren fasaha na cikin gida wajen amfani da albarkatun cikin gida domin kawo dauki ga shirin gwamnati na sake fasalta harkokin wuta a kasa” (Garba Abdullahi Bagwai)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Abba Kyari Ta Dakatar Da Bincikensa

Related

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

28 minutes ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

17 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

18 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

19 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

20 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

21 hours ago
Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Abba Kyari Ta Dakatar Da Bincikensa

LABARAI MASU NASABA

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.