• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Za Ta Gina Masana`antar Samar Da Kayan Samar Da Wuta Ta Hanyar Hasken Rana

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Najeriya Za Ta Gina Masana`antar Samar Da Kayan Samar Da Wuta Ta Hanyar Hasken Rana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya juma`a 24 ga watan nan ne mataimakin shugaban tarayyar Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo, ya jagoranci bikin aza harsashin ginin masana`antar samar da kayan sarrafa hasken rana, domin samar da wutar lantarki a jihar Nasarawa dake shiyyar arewa ta tsakiyar Najeriya.

Ita dai wannan masana`anta, wadda za ta lashe tsabar kudi har Dala biliyan 71.19, za ta kasance irin ta ta farko a yammacin Afrika baki daya idan har an kammala ta.

  • An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da aikin a garin Gora dake jihar ta Nasarawa, mataimakin shugaban kasa Farfessa Yemi Osinbajo ya ce kasancewar jihar ta Nasarawa tana da arzikin sinadaran da ake amfani da su wajen samar da falankin dake zuko hasken rana don sarrafawa zuwa wuta ya sanya gwamnatin tarayyar yanke shawarar kaddamar da wannan gagarumin aiki a jihar.

Ya ce matakin zai taimaka sosai wajen aza Najeriya cikin sahun kasashe makwafta da suke amfani da hanyoyin samar da wuta domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli.

Aikin kamar yadda mataimakin shugaban kasar ya fada zai gudana ne karkashin kulawar hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya wato NASENI har ila yau yana daya daga cikin kokarin gwamantin Najeriya wajen tabbatar da ganin ta kara fadada saka jarin ta a fagen samar da makamashi.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Kuma akwai kyakkywan fatan aikin zai iya kawo sauyi mai ma`ana ta fuskar sake fasalin wutar latarki da makamashi a Najeriya.

“Wannan masana`anta zata zo a lokacin da ya dace, inda ban da cin gajiyar ta da jama’a zasuyi, ta zo kuma daidai manufa da shirye shiryen kungiyar tarayyar Afrika ta amfani a sabbin hanyoyin samar da makamashi domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli, baya ga tasirin da za ta yi wajen kawo saukin farashin na`urorin samar da wuta ta hasken rana a Najeriya”

A nasa jawabin, shugaban hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya Farfesa Muhammad Haruna cewa yayi tun shekaru goma da suka gabata hukumar ta tsunduma cikin harkar samar da wuta ta amfani da makamashin solar a Najeriya.

“Hukumar NASENI karkashin jagoranci na da kuma gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari sun damu mutuka bisa yanayi wutar lantarki a Najeriya, wannan ce ta sa aka mayar da hankali wajen amfani da kimiya da kirkire-kirkiren fasaha na cikin gida wajen amfani da albarkatun cikin gida domin kawo dauki ga shirin gwamnati na sake fasalta harkokin wuta a kasa” (Garba Abdullahi Bagwai)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Abba Kyari Ta Dakatar Da Bincikensa

Related

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

10 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

11 hours ago
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

12 hours ago
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma
Daga Birnin Sin

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

13 hours ago
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
Daga Birnin Sin

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

14 hours ago
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

15 hours ago
Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Abba Kyari Ta Dakatar Da Bincikensa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.