ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Za Ta Gina Masana`antar Samar Da Kayan Samar Da Wuta Ta Hanyar Hasken Rana

by CMG Hausa
3 years ago
Hasken rana

A jiya juma`a 24 ga watan nan ne mataimakin shugaban tarayyar Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo, ya jagoranci bikin aza harsashin ginin masana`antar samar da kayan sarrafa hasken rana, domin samar da wutar lantarki a jihar Nasarawa dake shiyyar arewa ta tsakiyar Najeriya.

Ita dai wannan masana`anta, wadda za ta lashe tsabar kudi har Dala biliyan 71.19, za ta kasance irin ta ta farko a yammacin Afrika baki daya idan har an kammala ta.

  • An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da aikin a garin Gora dake jihar ta Nasarawa, mataimakin shugaban kasa Farfessa Yemi Osinbajo ya ce kasancewar jihar ta Nasarawa tana da arzikin sinadaran da ake amfani da su wajen samar da falankin dake zuko hasken rana don sarrafawa zuwa wuta ya sanya gwamnatin tarayyar yanke shawarar kaddamar da wannan gagarumin aiki a jihar.

ADVERTISEMENT

Ya ce matakin zai taimaka sosai wajen aza Najeriya cikin sahun kasashe makwafta da suke amfani da hanyoyin samar da wuta domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli.

Aikin kamar yadda mataimakin shugaban kasar ya fada zai gudana ne karkashin kulawar hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya wato NASENI har ila yau yana daya daga cikin kokarin gwamantin Najeriya wajen tabbatar da ganin ta kara fadada saka jarin ta a fagen samar da makamashi.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Kuma akwai kyakkywan fatan aikin zai iya kawo sauyi mai ma`ana ta fuskar sake fasalin wutar latarki da makamashi a Najeriya.

“Wannan masana`anta zata zo a lokacin da ya dace, inda ban da cin gajiyar ta da jama’a zasuyi, ta zo kuma daidai manufa da shirye shiryen kungiyar tarayyar Afrika ta amfani a sabbin hanyoyin samar da makamashi domin kawo karshen matsalolin dumamar yanayi da gurbatar muhalli, baya ga tasirin da za ta yi wajen kawo saukin farashin na`urorin samar da wuta ta hasken rana a Najeriya”

A nasa jawabin, shugaban hukumar kirkire-kirkiren fasaha ta Najeriya Farfesa Muhammad Haruna cewa yayi tun shekaru goma da suka gabata hukumar ta tsunduma cikin harkar samar da wuta ta amfani da makamashin solar a Najeriya.

“Hukumar NASENI karkashin jagoranci na da kuma gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari sun damu mutuka bisa yanayi wutar lantarki a Najeriya, wannan ce ta sa aka mayar da hankali wajen amfani da kimiya da kirkire-kirkiren fasaha na cikin gida wajen amfani da albarkatun cikin gida domin kawo dauki ga shirin gwamnati na sake fasalta harkokin wuta a kasa” (Garba Abdullahi Bagwai)

 

Hasken rana
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Abba Kyari Ta Dakatar Da Bincikensa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.