• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarar APC A Zaɓen Cike Gurbi Ta Tabbatar Da Sahihancin Mulkin Uba Sani – Mai Yaki

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan yada labarai na jihar Kaduna, Malam Ahmed Mai yaki ya mayar da martani ga nasarar da jam’iyyar APC ta samu a mazabar Dan majalisar wakilai na tarayya ta Chikun/Kajuru inda ya bayyana ta a matsayin sahihancin gwamnatin Gwamna Uba Sani da manufofinta na hada kan jama’a.

 

Mai yaki yana amsa tambayoyin manema labarai ne bayan bayyana sakamakon zaben mazabar kujerar dan majalisar wakilai na tarayya na Chikun/Kajuru da kuma mazabar Zariya Kewaye da Basawa.

  • An Yi Gwaji Na Biyu Na Bikin Tunawa Da Nasarar Sinawa A Yakin Kin Harin Japan 
  • Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Ya ce sakamakon ya nuna irin amincewar al’ummomin da ke Kaduna a yanzu a kan shugabancin Gwamna Uba Sani da kuma jam’iyya mai mulki, inda ya ce nasarar da aka samu “na tarihi ce da kuma alamta nasarorin gwamnatin APC.

 

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Ya bayyana cewa da wannan nasarar da jam’iyyar ta samu a jihar Kaduna, ya kara karfin ikonta zuwa yan kunan da aka ganin kamar suna karkashin ikon jam’iyyar adawa ne.

 

“A cewar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Jam’iyyar APC ta samu kuri’u 34,580 inda ta lallasa abokan hamayyarta da gaske. Jam’iyyar PDP, wacce a da ake kallonta a matsayin ‘yan adawa a Chikun da Kajuru, ta samu kuri’u 11,491 kacal, yayin da jam’iyyar (ADC) ta samu kuri’u 3,477. Jam’iyyar (SDP) ta biyo baya da kuri’u 142 kacal”

 

Mai yaki ya alakanta nasarorin da aka samu a kan jagorancin Gwamna Uba Sani wanda ya mayar da hankali a kai, wanda ya samar da kyakkyawan sakamako ta hanyar samar da ababen more rayuwa, sabunta harkokin kiwon lafiya, gyare-gyaren ilimi, da matakan tsaro – manufofin da suka yi tasiri sosai ga masu kada kuri’a da kuma share fagen samun gagarumar nasara.

 

“Al’ummar Chikun da Kajuru da Zariya Kewaye da Basawa sun yi magana da babbar murya – suna son shugabanci mai ci gaba, ba wai alkawuran da za a sake yin amfani da su ba, sun amince da salon jagorancin Gwamna Uba Sani na hada kai”

 

Mai yaki ya jaddada cewa jam’iyyar APC ba wai kawai ta karya wani sabon salo ba ne, har ma ta tabbatar da matsayinta na babbar jam’iyyar siyasa a jihar Kaduna.

 

Ya kara da cewa irin wannan gagarumin nasara da aka samu ya sanya jam’iyyar a kan turbar da ta dace kafin shekarar 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fim Na Kisan Kiyashin Da Sojojin Japan Suka Yi A Birnin Nanjing Na Samun Karbuwa A Kasar Sin

Next Post

Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

1 hour ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

3 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

8 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

10 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

11 hours ago
Next Post
Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.