• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarar APC A Zaɓen Cike Gurbi Ta Tabbatar Da Sahihancin Mulkin Uba Sani – Mai Yaki

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 months ago
Ruwa

Kwamishinan yada labarai na jihar Kaduna, Malam Ahmed Mai yaki ya mayar da martani ga nasarar da jam’iyyar APC ta samu a mazabar Dan majalisar wakilai na tarayya ta Chikun/Kajuru inda ya bayyana ta a matsayin sahihancin gwamnatin Gwamna Uba Sani da manufofinta na hada kan jama’a.

 

Mai yaki yana amsa tambayoyin manema labarai ne bayan bayyana sakamakon zaben mazabar kujerar dan majalisar wakilai na tarayya na Chikun/Kajuru da kuma mazabar Zariya Kewaye da Basawa.

  • An Yi Gwaji Na Biyu Na Bikin Tunawa Da Nasarar Sinawa A Yakin Kin Harin Japan 
  • Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Ya ce sakamakon ya nuna irin amincewar al’ummomin da ke Kaduna a yanzu a kan shugabancin Gwamna Uba Sani da kuma jam’iyya mai mulki, inda ya ce nasarar da aka samu “na tarihi ce da kuma alamta nasarorin gwamnatin APC.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

Ya bayyana cewa da wannan nasarar da jam’iyyar ta samu a jihar Kaduna, ya kara karfin ikonta zuwa yan kunan da aka ganin kamar suna karkashin ikon jam’iyyar adawa ne.

 

“A cewar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Jam’iyyar APC ta samu kuri’u 34,580 inda ta lallasa abokan hamayyarta da gaske. Jam’iyyar PDP, wacce a da ake kallonta a matsayin ‘yan adawa a Chikun da Kajuru, ta samu kuri’u 11,491 kacal, yayin da jam’iyyar (ADC) ta samu kuri’u 3,477. Jam’iyyar (SDP) ta biyo baya da kuri’u 142 kacal”

 

Mai yaki ya alakanta nasarorin da aka samu a kan jagorancin Gwamna Uba Sani wanda ya mayar da hankali a kai, wanda ya samar da kyakkyawan sakamako ta hanyar samar da ababen more rayuwa, sabunta harkokin kiwon lafiya, gyare-gyaren ilimi, da matakan tsaro – manufofin da suka yi tasiri sosai ga masu kada kuri’a da kuma share fagen samun gagarumar nasara.

 

“Al’ummar Chikun da Kajuru da Zariya Kewaye da Basawa sun yi magana da babbar murya – suna son shugabanci mai ci gaba, ba wai alkawuran da za a sake yin amfani da su ba, sun amince da salon jagorancin Gwamna Uba Sani na hada kai”

 

Mai yaki ya jaddada cewa jam’iyyar APC ba wai kawai ta karya wani sabon salo ba ne, har ma ta tabbatar da matsayinta na babbar jam’iyyar siyasa a jihar Kaduna.

 

Ya kara da cewa irin wannan gagarumin nasara da aka samu ya sanya jam’iyyar a kan turbar da ta dace kafin shekarar 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL
Manyan Labarai

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Next Post
Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.