• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarar APC A Zaɓen Cike Gurbi Ta Tabbatar Da Sahihancin Mulkin Uba Sani – Mai Yaki

by Shehu Yahaya and Sulaiman
4 weeks ago
in Labarai
0
Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan yada labarai na jihar Kaduna, Malam Ahmed Mai yaki ya mayar da martani ga nasarar da jam’iyyar APC ta samu a mazabar Dan majalisar wakilai na tarayya ta Chikun/Kajuru inda ya bayyana ta a matsayin sahihancin gwamnatin Gwamna Uba Sani da manufofinta na hada kan jama’a.

 

Mai yaki yana amsa tambayoyin manema labarai ne bayan bayyana sakamakon zaben mazabar kujerar dan majalisar wakilai na tarayya na Chikun/Kajuru da kuma mazabar Zariya Kewaye da Basawa.

  • An Yi Gwaji Na Biyu Na Bikin Tunawa Da Nasarar Sinawa A Yakin Kin Harin Japan 
  • Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Ya ce sakamakon ya nuna irin amincewar al’ummomin da ke Kaduna a yanzu a kan shugabancin Gwamna Uba Sani da kuma jam’iyya mai mulki, inda ya ce nasarar da aka samu “na tarihi ce da kuma alamta nasarorin gwamnatin APC.

 

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

Ya bayyana cewa da wannan nasarar da jam’iyyar ta samu a jihar Kaduna, ya kara karfin ikonta zuwa yan kunan da aka ganin kamar suna karkashin ikon jam’iyyar adawa ne.

 

“A cewar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Jam’iyyar APC ta samu kuri’u 34,580 inda ta lallasa abokan hamayyarta da gaske. Jam’iyyar PDP, wacce a da ake kallonta a matsayin ‘yan adawa a Chikun da Kajuru, ta samu kuri’u 11,491 kacal, yayin da jam’iyyar (ADC) ta samu kuri’u 3,477. Jam’iyyar (SDP) ta biyo baya da kuri’u 142 kacal”

 

Mai yaki ya alakanta nasarorin da aka samu a kan jagorancin Gwamna Uba Sani wanda ya mayar da hankali a kai, wanda ya samar da kyakkyawan sakamako ta hanyar samar da ababen more rayuwa, sabunta harkokin kiwon lafiya, gyare-gyaren ilimi, da matakan tsaro – manufofin da suka yi tasiri sosai ga masu kada kuri’a da kuma share fagen samun gagarumar nasara.

 

“Al’ummar Chikun da Kajuru da Zariya Kewaye da Basawa sun yi magana da babbar murya – suna son shugabanci mai ci gaba, ba wai alkawuran da za a sake yin amfani da su ba, sun amince da salon jagorancin Gwamna Uba Sani na hada kai”

 

Mai yaki ya jaddada cewa jam’iyyar APC ba wai kawai ta karya wani sabon salo ba ne, har ma ta tabbatar da matsayinta na babbar jam’iyyar siyasa a jihar Kaduna.

 

Ya kara da cewa irin wannan gagarumin nasara da aka samu ya sanya jam’iyyar a kan turbar da ta dace kafin shekarar 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fim Na Kisan Kiyashin Da Sojojin Japan Suka Yi A Birnin Nanjing Na Samun Karbuwa A Kasar Sin

Next Post

Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

Related

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

1 minute ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

1 hour ago
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu
Labarai

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

2 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

4 hours ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

5 hours ago
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna
Labarai

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

15 hours ago
Next Post
Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

Wang Yi Zai Ziyarci Indiya Da Gudanar Da Taron Wakilan Musamman Kan Batun Iyakar Sin Da Indiya Karo Na 24

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.