• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

by Abubakar Abba
9 months ago
in Labarai
0
Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan an gano danyen mai a 1950 Nijeria ne, aka fara yiwa fannin aikin noma na Nijeriya rkon Sakanr Kashi.

Fannin wanda na daya daga cikin gwagwarmayar da masu hakilon samun yancin kan kasar suka karfafa shi na kan gaba wajen habaka tattalin arzikin kasar.

  • Nazari Kan Gazawar Tsofaffin Ministocin Noma 52 Da Suka Shude A Nijeriya
  • Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

Kafin samun ‘yancin kan kasar, a 1950 Nijeriya ce kan gaba a duniya, wajen noma Kwakwar Manja da kuma Cocoa.

Hakazalika, fannin na samar da ayyukan yi da suka kai sama da kashi 70, wanda hakan ya kai kusan kashi 62.3 na kudaden musayar na shiga, da kasar ke samu.

Bisa wata kididdiga da aka samu daga gun bankin duniya ta nuna cewa, fanin na samar da sama da kashi 60, ga tattalin arzikin kasar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Sai dai, bayan gano danyen man a 1950, hakan ya janyo an yi watsi da fannin, wanda hakan ya sanya kimar Nijeiya a fannin aikin noma a fadin duniya, ta fadi warwas.

Amma domin a sake farfado da kimar Nijeriya a fannin, shugabannin da suka mulki kasar, sun kirkiro da tsare-tsaren aikin noma da ban da ban.

Sai dai, abun takaicin shi ne, wadannan tsare-tsaren, kusan za a iya cewa, ba su wani tasiri ba saboda sauye-sauyen shugabanci da aka samu a kasar.

 

Tsare-Tsaren Da Aka Kirkiro Bayan Samun ‘Yancin Kai:

Domin rage radadin yakin basasa a fanin aikin noma, tsohuwar gwamnatin mulkin soji ta Janar Yakubu Gowon mai murabus, ya kirkiro da tsarin NAFPP na kasa a 1972 don bunkasa samar da abinci, ta hanyar ilimantar da manoma.

An kaddamar da tsarin na gwaji a jihohin Anambra, Imo, Ondo, Oyo, Ogun, Benue, Filato da Kano.

Sai dai, tsarin ya ci karo da kalubale na rashin gazawar manoma na kafa kungiyoyi don a tallafa masu da kudaden aikin noma da sauran kayan aiki.

Hakazalika,a a 1973, Gowon ya kafa hukumar RBDA bisa nufin samar da kayan aikin noma rani, ta hanyar kakkafa Dam Dam don tara ruwan na noman rani.

Daga baya kuma a 1975ya kirkiro da aikin bunkasa aikin na noma ADP.

Bugu da kari, a lokacin tsohowar gwamnatin mulkin soji ta Cif Olusegun Obasanjo a 1976 bankin CBN, ya kirkiro da aikin habaka aikin noma na kasa OFN.

Manufar ita ce, don a kara yawan noma da ake yi a kasar, musamman don a samar da abinci, mai gina jiki.

Tsarin ya kai har 1979 na lokacin mulikin tsohowar gwamnatin farar hula ta marigayi Shehu Shagari.

A watan Afirilun 1980, Shagari ya kirkiro da tsarin farfado da aikin noma na GRP bisa nufin samar da wadataccen abinci ta hanyar yin amfani da fasahar zamani.

Bugu da kari, a 1986, lokacin tsohuwar mulkin soji ta tsohon shugaban kasa na mulkin soji Janar Ibrahim Badamasi Babangida mai murabus, ya kirkiro da tsarin DFRRI, bisa nufin tallafa wa alumomi.

 

Daga 1999 zuwa 2020:

Tsohohuwar gwamnatin farar hula ta tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo, a watan Afirilun 2003, ya kirkiro da tsarin aikin samar da wadataccen abinci na kasa NSPFS.

Ya kirkiro da tsarin don a taimaka wa manoma su samun karin kudaden shiga da karfafa ayyukan noman rani da sauransu.

Sai dai, tsarin ya ci karo da matsala saboda manoman da aka bai wa kudin rancen yin noma, sunki maido da kuadaden a kan lokaci tare da kuma kalubalen da manoman suka fuskanta na rashin yin amfani da kimiyyar fasahar noma.

A shekaru takwas na mulkin Obasanjo, fannin ya bayar da gudunamawa na bunkasa tattalin arzikin kasar.

Har ila yau, a lokacin tsohuwar mulkin marigayi shugaban kasa Umaru Yar’Adua, ya kirkiro da tsarin ajanda bakwai da kuma shirin habaka aikin noma na kasa NFSP.

Manufar shirin ya hada da; bayar da kudaden hadaka na aikin noma na FADAMA III; IFAD da ayyuan bunkasa aikin noma na ADB da sauransu.

Yar’Adua, ya bayar da gagarumar gudunmawa ga tattalin arzikin kasar wadda ta kai kashi 25.31.

Bugu da kari, a 2011, tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya kaddamar da tsarin aikin noma na ATA.

Ya kirkiro da tsarin ne, domin a habaka noman, musamman kanaanan manoma wanda kimanin kanannan manoma 45,300 da ke a karkara suka amfana.

A lokacin, fannin ya taimaka da wajen kashi 21.09 ga tattalin arzikin kasar.

Hakazalika, a lokacin mulkin tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa na mulkin dimokiradayya Muhammadu Buhari a shekarar 2015, ya kirkiro da tsarin habaka aikin noma na APP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarmingNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

Next Post

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

6 hours ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

8 hours ago
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
Labarai

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

9 hours ago
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
Labarai

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

10 hours ago
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

12 hours ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

13 hours ago
Next Post
Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.