• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

by Abubakar Abba
11 months ago
in Labarai
0
Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan an gano danyen mai a 1950 Nijeria ne, aka fara yiwa fannin aikin noma na Nijeriya rkon Sakanr Kashi.

Fannin wanda na daya daga cikin gwagwarmayar da masu hakilon samun yancin kan kasar suka karfafa shi na kan gaba wajen habaka tattalin arzikin kasar.

  • Nazari Kan Gazawar Tsofaffin Ministocin Noma 52 Da Suka Shude A Nijeriya
  • Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

Kafin samun ‘yancin kan kasar, a 1950 Nijeriya ce kan gaba a duniya, wajen noma Kwakwar Manja da kuma Cocoa.

Hakazalika, fannin na samar da ayyukan yi da suka kai sama da kashi 70, wanda hakan ya kai kusan kashi 62.3 na kudaden musayar na shiga, da kasar ke samu.

Bisa wata kididdiga da aka samu daga gun bankin duniya ta nuna cewa, fanin na samar da sama da kashi 60, ga tattalin arzikin kasar.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

Sai dai, bayan gano danyen man a 1950, hakan ya janyo an yi watsi da fannin, wanda hakan ya sanya kimar Nijeiya a fannin aikin noma a fadin duniya, ta fadi warwas.

Amma domin a sake farfado da kimar Nijeriya a fannin, shugabannin da suka mulki kasar, sun kirkiro da tsare-tsaren aikin noma da ban da ban.

Sai dai, abun takaicin shi ne, wadannan tsare-tsaren, kusan za a iya cewa, ba su wani tasiri ba saboda sauye-sauyen shugabanci da aka samu a kasar.

 

Tsare-Tsaren Da Aka Kirkiro Bayan Samun ‘Yancin Kai:

Domin rage radadin yakin basasa a fanin aikin noma, tsohuwar gwamnatin mulkin soji ta Janar Yakubu Gowon mai murabus, ya kirkiro da tsarin NAFPP na kasa a 1972 don bunkasa samar da abinci, ta hanyar ilimantar da manoma.

An kaddamar da tsarin na gwaji a jihohin Anambra, Imo, Ondo, Oyo, Ogun, Benue, Filato da Kano.

Sai dai, tsarin ya ci karo da kalubale na rashin gazawar manoma na kafa kungiyoyi don a tallafa masu da kudaden aikin noma da sauran kayan aiki.

Hakazalika,a a 1973, Gowon ya kafa hukumar RBDA bisa nufin samar da kayan aikin noma rani, ta hanyar kakkafa Dam Dam don tara ruwan na noman rani.

Daga baya kuma a 1975ya kirkiro da aikin bunkasa aikin na noma ADP.

Bugu da kari, a lokacin tsohowar gwamnatin mulkin soji ta Cif Olusegun Obasanjo a 1976 bankin CBN, ya kirkiro da aikin habaka aikin noma na kasa OFN.

Manufar ita ce, don a kara yawan noma da ake yi a kasar, musamman don a samar da abinci, mai gina jiki.

Tsarin ya kai har 1979 na lokacin mulikin tsohowar gwamnatin farar hula ta marigayi Shehu Shagari.

A watan Afirilun 1980, Shagari ya kirkiro da tsarin farfado da aikin noma na GRP bisa nufin samar da wadataccen abinci ta hanyar yin amfani da fasahar zamani.

Bugu da kari, a 1986, lokacin tsohuwar mulkin soji ta tsohon shugaban kasa na mulkin soji Janar Ibrahim Badamasi Babangida mai murabus, ya kirkiro da tsarin DFRRI, bisa nufin tallafa wa alumomi.

 

Daga 1999 zuwa 2020:

Tsohohuwar gwamnatin farar hula ta tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo, a watan Afirilun 2003, ya kirkiro da tsarin aikin samar da wadataccen abinci na kasa NSPFS.

Ya kirkiro da tsarin don a taimaka wa manoma su samun karin kudaden shiga da karfafa ayyukan noman rani da sauransu.

Sai dai, tsarin ya ci karo da matsala saboda manoman da aka bai wa kudin rancen yin noma, sunki maido da kuadaden a kan lokaci tare da kuma kalubalen da manoman suka fuskanta na rashin yin amfani da kimiyyar fasahar noma.

A shekaru takwas na mulkin Obasanjo, fannin ya bayar da gudunamawa na bunkasa tattalin arzikin kasar.

Har ila yau, a lokacin tsohuwar mulkin marigayi shugaban kasa Umaru Yar’Adua, ya kirkiro da tsarin ajanda bakwai da kuma shirin habaka aikin noma na kasa NFSP.

Manufar shirin ya hada da; bayar da kudaden hadaka na aikin noma na FADAMA III; IFAD da ayyuan bunkasa aikin noma na ADB da sauransu.

Yar’Adua, ya bayar da gagarumar gudunmawa ga tattalin arzikin kasar wadda ta kai kashi 25.31.

Bugu da kari, a 2011, tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya kaddamar da tsarin aikin noma na ATA.

Ya kirkiro da tsarin ne, domin a habaka noman, musamman kanaanan manoma wanda kimanin kanannan manoma 45,300 da ke a karkara suka amfana.

A lokacin, fannin ya taimaka da wajen kashi 21.09 ga tattalin arzikin kasar.

Hakazalika, a lokacin mulkin tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa na mulkin dimokiradayya Muhammadu Buhari a shekarar 2015, ya kirkiro da tsarin habaka aikin noma na APP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarmingNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

Next Post

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Related

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

2 minutes ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

3 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

3 hours ago
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya
Labarai

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

7 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

16 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

17 hours ago
Next Post
Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.