ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

by Abubakar Abba
2 years ago
Noma

Bayan an gano danyen mai a 1950 Nijeria ne, aka fara yiwa fannin aikin noma na Nijeriya rkon Sakanr Kashi.

Fannin wanda na daya daga cikin gwagwarmayar da masu hakilon samun yancin kan kasar suka karfafa shi na kan gaba wajen habaka tattalin arzikin kasar.

  • Nazari Kan Gazawar Tsofaffin Ministocin Noma 52 Da Suka Shude A Nijeriya
  • Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

Kafin samun ‘yancin kan kasar, a 1950 Nijeriya ce kan gaba a duniya, wajen noma Kwakwar Manja da kuma Cocoa.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, fannin na samar da ayyukan yi da suka kai sama da kashi 70, wanda hakan ya kai kusan kashi 62.3 na kudaden musayar na shiga, da kasar ke samu.

Bisa wata kididdiga da aka samu daga gun bankin duniya ta nuna cewa, fanin na samar da sama da kashi 60, ga tattalin arzikin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sai dai, bayan gano danyen man a 1950, hakan ya janyo an yi watsi da fannin, wanda hakan ya sanya kimar Nijeiya a fannin aikin noma a fadin duniya, ta fadi warwas.

Amma domin a sake farfado da kimar Nijeriya a fannin, shugabannin da suka mulki kasar, sun kirkiro da tsare-tsaren aikin noma da ban da ban.

Sai dai, abun takaicin shi ne, wadannan tsare-tsaren, kusan za a iya cewa, ba su wani tasiri ba saboda sauye-sauyen shugabanci da aka samu a kasar.

 

Tsare-Tsaren Da Aka Kirkiro Bayan Samun ‘Yancin Kai:

Domin rage radadin yakin basasa a fanin aikin noma, tsohuwar gwamnatin mulkin soji ta Janar Yakubu Gowon mai murabus, ya kirkiro da tsarin NAFPP na kasa a 1972 don bunkasa samar da abinci, ta hanyar ilimantar da manoma.

An kaddamar da tsarin na gwaji a jihohin Anambra, Imo, Ondo, Oyo, Ogun, Benue, Filato da Kano.

Sai dai, tsarin ya ci karo da kalubale na rashin gazawar manoma na kafa kungiyoyi don a tallafa masu da kudaden aikin noma da sauran kayan aiki.

Hakazalika,a a 1973, Gowon ya kafa hukumar RBDA bisa nufin samar da kayan aikin noma rani, ta hanyar kakkafa Dam Dam don tara ruwan na noman rani.

Daga baya kuma a 1975ya kirkiro da aikin bunkasa aikin na noma ADP.

Bugu da kari, a lokacin tsohowar gwamnatin mulkin soji ta Cif Olusegun Obasanjo a 1976 bankin CBN, ya kirkiro da aikin habaka aikin noma na kasa OFN.

Manufar ita ce, don a kara yawan noma da ake yi a kasar, musamman don a samar da abinci, mai gina jiki.

Tsarin ya kai har 1979 na lokacin mulikin tsohowar gwamnatin farar hula ta marigayi Shehu Shagari.

A watan Afirilun 1980, Shagari ya kirkiro da tsarin farfado da aikin noma na GRP bisa nufin samar da wadataccen abinci ta hanyar yin amfani da fasahar zamani.

Bugu da kari, a 1986, lokacin tsohuwar mulkin soji ta tsohon shugaban kasa na mulkin soji Janar Ibrahim Badamasi Babangida mai murabus, ya kirkiro da tsarin DFRRI, bisa nufin tallafa wa alumomi.

 

Daga 1999 zuwa 2020:

Tsohohuwar gwamnatin farar hula ta tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo, a watan Afirilun 2003, ya kirkiro da tsarin aikin samar da wadataccen abinci na kasa NSPFS.

Ya kirkiro da tsarin don a taimaka wa manoma su samun karin kudaden shiga da karfafa ayyukan noman rani da sauransu.

Sai dai, tsarin ya ci karo da matsala saboda manoman da aka bai wa kudin rancen yin noma, sunki maido da kuadaden a kan lokaci tare da kuma kalubalen da manoman suka fuskanta na rashin yin amfani da kimiyyar fasahar noma.

A shekaru takwas na mulkin Obasanjo, fannin ya bayar da gudunamawa na bunkasa tattalin arzikin kasar.

Har ila yau, a lokacin tsohuwar mulkin marigayi shugaban kasa Umaru Yar’Adua, ya kirkiro da tsarin ajanda bakwai da kuma shirin habaka aikin noma na kasa NFSP.

Manufar shirin ya hada da; bayar da kudaden hadaka na aikin noma na FADAMA III; IFAD da ayyuan bunkasa aikin noma na ADB da sauransu.

Yar’Adua, ya bayar da gagarumar gudunmawa ga tattalin arzikin kasar wadda ta kai kashi 25.31.

Bugu da kari, a 2011, tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya kaddamar da tsarin aikin noma na ATA.

Ya kirkiro da tsarin ne, domin a habaka noman, musamman kanaanan manoma wanda kimanin kanannan manoma 45,300 da ke a karkara suka amfana.

A lokacin, fannin ya taimaka da wajen kashi 21.09 ga tattalin arzikin kasar.

Hakazalika, a lokacin mulkin tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa na mulkin dimokiradayya Muhammadu Buhari a shekarar 2015, ya kirkiro da tsarin habaka aikin noma na APP.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.