• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kama Wasu ’Yan Kwaya 4 Da Ake Nema Ruwa A Jallo Kan Mu’amala Da Miyagun Kwayoyi

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Kama Wasu ’Yan Kwaya 4 Da Ake Nema Ruwa A Jallo Kan Mu’amala Da Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA), ta kama wasu mata biyu da wasu maza biyu da ake nema ruwa a jallo bisa zarginsu da laifin safarar miyagun kwayoyi sama da kilogiram 16,000 da aka kama a Legas, Abuja da kuma Netherlands.

Kakakin hukumar NDLEA, Femi Babafemi, ya ce a Legas jami’an yaki da muggan kwayoyi sun shafe makonni suna bin diddigin, Aro Aderinde mai shekaru 48, sun kama shi a ranar Lahadi 16 ga watan Oktoba, bisa zarginsa da hannu wajen fitar da tabar wiwi kilogiram 3,149 da aka boye a cikin kwakwa, mai lambar kwantena MSKU 1820587.

  • NDLEA Ta Damke Mutum 345 Bisa Zargin Ta’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Katsina
  • NDLEA Ta Cafke Mai Juna Biyu Da Dalibin Jami’a Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

Haka kuma, an kama wasu mata biyu: Hauwawu Bashiru da Basirat Adebisi Yahaya kan yunkurin fitar da kilogiram 90 na methamphetamine zuwa kasashen waje ta hannun Fasto Anietie Okon Effiong na Cocin Promise of Zion Church, Oron, jihar Akwa Ibom, kamar yadda aka kama a Legas kuma aka koma Uyo don fuskantar tuhuma tare da limamin cocin.

Ku tuna cewa tun farko an kama Fasto Effiong a ranar Asabar 6 ga Agusta, 2022.

Wani da ake zargi da laifin safarar miyagun kwayoyi, Abdulkadir Mohammed, mai shekaru 47, wanda ake nema ruwa a jallo bisa kama shi da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 5,640 a wani dakin ajiya da ke unguwar Chukuku a Kuje, Abuja, a ranar Lahadi 16 ga watan Oktoba, bayan kama matarsa, Saadatu Abdullahi, mai shekaru 35, wadda ta kasance an same shi a kantin lokacin da aka kai samamen.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

A halin da ake ciki kuma, an kama wani fitaccen mai sayar da magunguna a unguwar Mushin-Isolo ta Legas, Monday Michael, mai shekaru 45, a ranar Litinin 17 ga watan Oktoba, yayin da gano jigilar kilogiram 365.7 na tabar wiwi a cikin motoci kirar Toyota Sienna guda biyu masu lamba FST 189 FD da FST 273 GF.

A jihar Edo, an kama akalla mutane 10 da ake zargi da hannu wajen kama tabar wiwi mai nauyin kilogiram 4,870.2 a sassan jihar.

A ranar Laraba 19 ga watan Oktoba, jami’an tsaro sun kai farmaki kan iyakar dajin Ohusu, karamar hukumar Ovia ta kudu maso yammacin kasar inda suka kwato jimillar kilogiram 3,159.7 tare da kama mutane uku: Effiong Udo; Daniel Asuquo Ebong da Asuquo Effiong.

Hakazalika, a ranar Asabar, 22 ga watan Oktoba, jami’an ‘yan sanda sun kama wata motar kirar Toyota Sienna ta sararin samaniya dauke da buhu 49 na C/S mai nauyin kilogiram 638.5 a kan titin Owenusi a karamar hukumar Uhunmonde, yayin da aka kwato kilo 36 na abu daya da aka ajiye a cikin daji dake kan titin Uromi/Ubiaja.

A wani farmakin kuma an kama mutane uku da ake zargi da suka hada da John Paul, Liberty Rolland, da Aboki Stephen a Okpe da ke Akoko Edo dauke da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 55.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Karramawar Shugaban Kasa Ta Kara Min Ƙaimi – Sadiya Farouq

Next Post

Xi Ya Jaddada Fa’idar Babban Taron Wakilan JKS Na 20

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

9 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

10 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

11 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

12 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

12 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

12 hours ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Fa’idar Babban Taron Wakilan JKS Na 20

Xi Ya Jaddada Fa’idar Babban Taron Wakilan JKS Na 20

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.