• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Neco

Binciken PREMIUM TIMES ya tabbatar cewa jihar Kano ba ta zama jiha ta farko ba wajen samun sakamakon jarrabawar kammala Sakandare SSCE da Hukumar NECO ta fitar a 2025 ba, saɓanin iƙirarin da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi.

Gwamnan ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa Kano ta zama jiha mafi samun sakamakon mai kyau a, yana danganta hakan da manufofin gwamnatinsa a fannin ilimi. Ya ƙara da cewa Lagos da Oyo sun zo na biyu da na uku. Sai dai bayanai daga NECO sun nuna akasin haka, inda fiye da rabin daliban Kano suka kasa samun sakamako mai kyau.

Neco

Bisa ga alƙalumman NECO, cikin ɗalibai 136,762 da suka yi jarrabawar daga Kano, kashi 49.84% kacal ne suka samu mafi ƙarancin CREDIT biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi, yayinda kashi 50.16% suka gaza. Wannan ya sa Kano ta zo matsayi na 29 daga jihohi 37, inda kawai ta fi jihohin Arewa guda takwas kamar Yobe, da Adamawa, da Filato, da Borno, da Jigawa, da Katsina, da Zamfara da kuma Sokoto.

  • Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
  • Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura

A haƙiƙanin gaskiya, Abia ce ta fi kowa nasar a jadawalin jahohin, inda kashi 83.31% daga cikin dalibai 11,260 suka samu mafi ƙarancin CREDIT biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi. Jihohin Imo (83.09%), da Ebonyi (80.60%), da Anambra (76.80%) suna bin sahu. Kano ba ta cikin jerin jihohi goma na farko, sai dai tana cikin goman ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

Alƙalumman sun nuna cewa abin da Kano ta fi kowa da shi, shi ne yawan ɗalibai da suka rubuta jarrabawar, ba nasara ba. Duk da yake Kano ta samu ɗalibai 68,159 da suka yi nasara, an samu ɗalibai 68,603 da suka faɗi – hakan na nuna cewa Kano ta fi da yawan waɗanda suka gaza samun CREDIT 5 fiye da waɗanda suka yi nasara .

Wannan ya tabbatar da cewa iƙirarin gwamnan na Kano ya dogara ne kan adadin masu rubuta jarrabawar, ba ainihin waɗanda suka samu nasara ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Manyan Labarai

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Next Post
Goron Sallah

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.