• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEMA Ta Raba Tallafi Ga ‘Yan Hijira 24,000 A Katsina

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NEMA

Babban Jami’in Bayar da Tallafi da Tsugunarwa na Hukumar NEMA a Shiyyar Arewa Maso Yamma da ke Kaduna, Kasimu Muhammad Jere yana jawabi ga ‘yan gudun hijira yayin miƙa kayan tallafin a madadin Darakta Janar na NEMA a ƙaramar Hukumar Jibiya, a ranar 17 ga Yulin 2022

Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta raba kayan tallafin ga ‘yan gudun hijira 24,000 da ɓarnar ‘yan bindiga ta shafa a ƙananan Hukumomin Jibiya da Mani da ke Jihar Katsina.

  • Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Kayan tallafin da hukumar ta raba sun haɗa da abinci, buhunan shinkafa masu nauyin kilogiram 10 guda 13,000, da katan na tumatir 120, da katan na sinadarin ɗanɗanon girki 120, da jarkunan man girki mai cin lita 20 guda 120 da kuma buhunan gishiri mai nauyin kilogiram 20 guda 120.

Da yake jawabi a yayin rabon kayan, Darakta Janar na NEMA Mustapha Habib Ahmed wanda Babban Jami’in Bayar da Tallafi da Tsugunarwa na Hukumar a Shiyyar Arewa Maso Yamma da ke Kaduna, Kasimu Muhammad Jere ya wakilta, ya yi bayanin cewa tallafin wani ɓangare ne na taimakon da NEMA ke bayarwa a madadin Gwamnatin Tarayya domin rage wa mutanen da suka rasa matsugunansu raɗaɗin da suke ji.

A jawabinsa a madadin Gwamnatin Jihar Katsina, Babban Daraktan Hukumar Bayar da Tallafin Gaggawa ta Jihar (SEMA), wanda wani Darakta a hukumar, Yunusa Mahuta ya wakilta, ya yaba wa NEMA bisa karamcin da ta yi, tare da isar da godiyar gwamnatin jihar.

Da yake mayar da jawabi a madadin ‘yan gudun hijira a Ƙaramar Hukumar Mani, ɗan majalisar da ke wakiltar yankin a Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Alhaji Aminu Ashiru Mani ya yi godiya ta musamman ga NEMA bisa bayar da tallafin.

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Har ila yau, shi ma wani shugaban al’umma da ya yi magana a madadin ‘yan gudun hijira na Ƙaramar Hukumar Jibiya, Alhaji Kabiru Mashe, ya gode wa Gwamnatin Tarayya bisa yadda ta dube su da idon rahama ta hannun NEMA.

  • https://leadership.ng/we-worked-with-frsc-to-manage-road-traffic-during-sallah-celebration-nema/

Tallafin kayan dai na NEMA an raba wa ‘yan gudun hijira da ke garuruwan Shimdiɗa, Garin Mai Wuya, Tsambe, Garin Zango da Kwari da ke Ƙananan Hukumomin Jibiya da Mani a Jihar Katsina.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Next Post
INEC Ta Mayar Wa Davido Martani Kan Bai Wa Adeleke Takardar Shaidar Lashe Zabe

INEC Ta Mayar Wa Davido Martani Kan Bai Wa Adeleke Takardar Shaidar Lashe Zabe

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.