ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEMA Ta Raba Tallafi Ga ‘Yan Hijira 24,000 A Katsina

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
NEMA

Babban Jami’in Bayar da Tallafi da Tsugunarwa na Hukumar NEMA a Shiyyar Arewa Maso Yamma da ke Kaduna, Kasimu Muhammad Jere yana jawabi ga ‘yan gudun hijira yayin miƙa kayan tallafin a madadin Darakta Janar na NEMA a ƙaramar Hukumar Jibiya, a ranar 17 ga Yulin 2022

Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta raba kayan tallafin ga ‘yan gudun hijira 24,000 da ɓarnar ‘yan bindiga ta shafa a ƙananan Hukumomin Jibiya da Mani da ke Jihar Katsina.

  • Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Kayan tallafin da hukumar ta raba sun haɗa da abinci, buhunan shinkafa masu nauyin kilogiram 10 guda 13,000, da katan na tumatir 120, da katan na sinadarin ɗanɗanon girki 120, da jarkunan man girki mai cin lita 20 guda 120 da kuma buhunan gishiri mai nauyin kilogiram 20 guda 120.

Da yake jawabi a yayin rabon kayan, Darakta Janar na NEMA Mustapha Habib Ahmed wanda Babban Jami’in Bayar da Tallafi da Tsugunarwa na Hukumar a Shiyyar Arewa Maso Yamma da ke Kaduna, Kasimu Muhammad Jere ya wakilta, ya yi bayanin cewa tallafin wani ɓangare ne na taimakon da NEMA ke bayarwa a madadin Gwamnatin Tarayya domin rage wa mutanen da suka rasa matsugunansu raɗaɗin da suke ji.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa a madadin Gwamnatin Jihar Katsina, Babban Daraktan Hukumar Bayar da Tallafin Gaggawa ta Jihar (SEMA), wanda wani Darakta a hukumar, Yunusa Mahuta ya wakilta, ya yaba wa NEMA bisa karamcin da ta yi, tare da isar da godiyar gwamnatin jihar.

Da yake mayar da jawabi a madadin ‘yan gudun hijira a Ƙaramar Hukumar Mani, ɗan majalisar da ke wakiltar yankin a Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Alhaji Aminu Ashiru Mani ya yi godiya ta musamman ga NEMA bisa bayar da tallafin.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Har ila yau, shi ma wani shugaban al’umma da ya yi magana a madadin ‘yan gudun hijira na Ƙaramar Hukumar Jibiya, Alhaji Kabiru Mashe, ya gode wa Gwamnatin Tarayya bisa yadda ta dube su da idon rahama ta hannun NEMA.

  • https://leadership.ng/we-worked-with-frsc-to-manage-road-traffic-during-sallah-celebration-nema/

Tallafin kayan dai na NEMA an raba wa ‘yan gudun hijira da ke garuruwan Shimdiɗa, Garin Mai Wuya, Tsambe, Garin Zango da Kwari da ke Ƙananan Hukumomin Jibiya da Mani a Jihar Katsina.

 

NEMA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
INEC Ta Mayar Wa Davido Martani Kan Bai Wa Adeleke Takardar Shaidar Lashe Zabe

INEC Ta Mayar Wa Davido Martani Kan Bai Wa Adeleke Takardar Shaidar Lashe Zabe

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.