ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEMA Ta Raba Tallafi Ga ‘Yan Hijira 24,000 A Katsina

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
NEMA

Babban Jami’in Bayar da Tallafi da Tsugunarwa na Hukumar NEMA a Shiyyar Arewa Maso Yamma da ke Kaduna, Kasimu Muhammad Jere yana jawabi ga ‘yan gudun hijira yayin miƙa kayan tallafin a madadin Darakta Janar na NEMA a ƙaramar Hukumar Jibiya, a ranar 17 ga Yulin 2022

Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta raba kayan tallafin ga ‘yan gudun hijira 24,000 da ɓarnar ‘yan bindiga ta shafa a ƙananan Hukumomin Jibiya da Mani da ke Jihar Katsina.

  • Sojoji Sun Sake Ceto Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok A Borno

Kayan tallafin da hukumar ta raba sun haɗa da abinci, buhunan shinkafa masu nauyin kilogiram 10 guda 13,000, da katan na tumatir 120, da katan na sinadarin ɗanɗanon girki 120, da jarkunan man girki mai cin lita 20 guda 120 da kuma buhunan gishiri mai nauyin kilogiram 20 guda 120.

Da yake jawabi a yayin rabon kayan, Darakta Janar na NEMA Mustapha Habib Ahmed wanda Babban Jami’in Bayar da Tallafi da Tsugunarwa na Hukumar a Shiyyar Arewa Maso Yamma da ke Kaduna, Kasimu Muhammad Jere ya wakilta, ya yi bayanin cewa tallafin wani ɓangare ne na taimakon da NEMA ke bayarwa a madadin Gwamnatin Tarayya domin rage wa mutanen da suka rasa matsugunansu raɗaɗin da suke ji.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa a madadin Gwamnatin Jihar Katsina, Babban Daraktan Hukumar Bayar da Tallafin Gaggawa ta Jihar (SEMA), wanda wani Darakta a hukumar, Yunusa Mahuta ya wakilta, ya yaba wa NEMA bisa karamcin da ta yi, tare da isar da godiyar gwamnatin jihar.

Da yake mayar da jawabi a madadin ‘yan gudun hijira a Ƙaramar Hukumar Mani, ɗan majalisar da ke wakiltar yankin a Majalisar Wakilai ta Ƙasa, Alhaji Aminu Ashiru Mani ya yi godiya ta musamman ga NEMA bisa bayar da tallafin.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Har ila yau, shi ma wani shugaban al’umma da ya yi magana a madadin ‘yan gudun hijira na Ƙaramar Hukumar Jibiya, Alhaji Kabiru Mashe, ya gode wa Gwamnatin Tarayya bisa yadda ta dube su da idon rahama ta hannun NEMA.

  • https://leadership.ng/we-worked-with-frsc-to-manage-road-traffic-during-sallah-celebration-nema/

Tallafin kayan dai na NEMA an raba wa ‘yan gudun hijira da ke garuruwan Shimdiɗa, Garin Mai Wuya, Tsambe, Garin Zango da Kwari da ke Ƙananan Hukumomin Jibiya da Mani a Jihar Katsina.

 

NEMA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
INEC Ta Mayar Wa Davido Martani Kan Bai Wa Adeleke Takardar Shaidar Lashe Zabe

INEC Ta Mayar Wa Davido Martani Kan Bai Wa Adeleke Takardar Shaidar Lashe Zabe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.