• English
  • Business News
Thursday, October 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

by Rabilu Sanusi Bena
3 weeks ago
in Wasanni
0
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Talata, Super Eagles za su fafata da Bafana-Bafana na Afirka Ta Kudu a garin Bloemfontein, wasan zagaye na 8 na neman gurbin shiga gasar cin Kofin Duniya a rukuni na C.

Wannan wasa na da matuƙar muhimmanci ga Nijeriya wadda take matsayi na uku a rukuni, domin tana buƙatar nasara don ci gaba da fatan zuwa gasar a baɗi.

  • Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye
  • El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

A yanzu haka, Afirka Ta Kudu na gaba da Nijeriya da maki shida.

Sai dai akwai batun zabtare mata maki saboda zargin saka Teboho Mokoena a wasa duk da yana da jan kati sau biyu.

Idan hakan ta tabbata, tazarar maki tsakanin ƙasashen biyu na iya raguwa daga shida zuwa uku.

Labarai Masu Nasaba

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

Idan Afirka Ta Kudu ta yi nasara yau, za ta tabbatar da zuwa gasar Kofin Duniya da za a buga a Arewacin Amurka a 2026, kuma karo na farko tun bayan 2010 lokacin da ta ɗauki nauyin gasar.

Nijeriya kuwa, wadda ta halarci gasar sau shida a baya, tana ƙoƙarin dawo da martabarta.

Nasarar da ta samu a kan Rwanda a wasan da ya gabata ta farfaɗo da ƙwarin guiwar masoyanta, duk da cewa a wasanni bakwai da ta buga na neman gurbin shiga 2026, sau biyu kacal ta ci.

Wasan na yau shi ne karo na 17 da ƙasashen biyu za su haɗu.

Nijeriya ta fi samun nasara sau takwas, inda aka tashi canjaras sau bakwai, sai Afirka Ta Kudu da ta yi nasara sau 2 kacal.

Ana jiran a ga ko Bafana-Bafana za su ƙara daurewa, ko kuma Super Eagles za su ƙwato matsayinsu a cikin manyan ƙasashen ƙwallon ƙafa na duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Afrika Ta KuduƙwalloNijeriyaSuper EaglesWasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Next Post

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Related

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

1 day ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

2 days ago
Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku
Wasanni

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

3 days ago
Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad
Wasanni

Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

4 days ago
Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta
Wasanni

Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

4 days ago
Gwamna Makinde Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Nijeriya da Naira Miliyan 22
Wasanni

Gwamna Makinde Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Nijeriya da Naira Miliyan 22

4 days ago
Next Post
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

October 2, 2025
Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Tallafawa Ɗalibai 16,756 Da Naira Miliyan 592

Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Tallafawa Ɗalibai 16,756 Da Naira Miliyan 592

October 2, 2025
Gwamna Lawal Ya Gwangwaje Kamfanin Sufurin Mota Na Zamfara Da Motoci 50 

Gwamna Lawal Ya Gwangwaje Kamfanin Sufurin Mota Na Zamfara Da Motoci 50 

October 2, 2025
Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

October 2, 2025
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

October 2, 2025
Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

October 2, 2025
‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

‘Yansanda Sun Ƙwato Muggan Ƙwayoyi Na Naira Miliyan 120 A Kano

October 2, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

October 2, 2025
Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

Alaafin Ya Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Kama Masu Kashe Kashe A Kwara

October 2, 2025
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

October 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.