• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nesa Ta Zo Kusa a Afrika Karkashin Taimakon Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afrika

“Abin alfahari ne gare ni kasancewar na zama mace ta farko dake iya tuka jirgin kasa. Kamfanin Sin ya kyautata rayuwata”. Issa Fatima Abiola wadda ta sanyawa kan ta sunan “Baiyang” a Sinanci, ta bayyana hakan yayin da na zanta da ita a shekarar 2021. Ita ce mace mai tuka jirgin kasa ta farko a Najeriya, bayan kamfanin Sin ya horas da ita, matakin da ya kyautata rayuwarta matuka.

 

A halin yanzu, Issa Fatima Abiola, tana iya tuka jirgin kasa bayan horon da kamfanin Sin ya ba ta.

  • Kakakin Ma’aiktar Tsaron Sin Ya Gabatar Da Yadda Aka Gudanar Da Atisayen Hadin Gwiwa Na Sojojin Sin Da Tanzaniya Da Mozambique
  • Sin Da Afirka Aminai Ne Wajen Neman Zamanantar Da Kansu

A daya bangaren kuma, masu aikin jiyya da Sin da Comoros suka yi hadin gwiwa wajen horar da su, suna ceton rayukan mutane da dama daga cutar zazzabin cizon sauro. Kana matasan Tanzaniya da suka yi karatu a Sin suna kokarin yada fasahohin noma na zamani a kasarsu. A gare su nesa ta zo kusa a rayuwar su, karkashin hadin gwiwar Sin da Afrika a fannin daga karfin samun bunkasuwa bisa dogaro da kansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Sinawa kan cewa “Guntun gatarinka ya fi sari ka ba ni”, saboda haka a ganinsu abu mafi muhimmanci shi ne taimakawa kasashe masu tasowa ciki har da kasashen Afirka, da karfin samun bunkasuwa ta hanyar dogaro da kai. Hakan ya sa kasar Sin gabatar da shirin hadin gwiwa da Afrika kan wasu manyan ayyuka 9, ciki har da aikin nan na daga karfin samun ci gaba, a gun taron ministoci karo na 8 na dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afrika da aka gudanar a watan Nuwamban shekarar 2021.

 

Hadin gwiwar Sin da Afrika, wajen daga karfin samun bunkasuwa ta hanyar dogaro da kai, na dora muhimmanci sosai kan ainihin bukatun Afirka, lamarin da ya cika burin jama’a, kuma yake bunkasa hadin gwiwarsu don samun ci gaban Afrika mai inganci. (Mai zane da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

October 12, 2025
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Jinjina Wa Kamfanin Ɗangote Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasa

Majalisar Wakilai Ta Jinjina Wa Kamfanin Ɗangote Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.