• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar Ta Cika Shekaru 65 Da Samun ‘Yancin Kai

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Nijar Ta Cika Shekaru 65 Da Samun ‘Yancin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar, ya jinjina wa al’ummar kasar saboda yadda suka jurewa matsalolin da suka biyo bayan takunkumin kungiyar CEDEAO da UEMOA.

A yayin da a ranar Litinin 18 ga watan Disamba kasar Nijar ke bukukuwan cika shekaru 65 da zama jamhuriya, shugaban gwamnatin mulkin sojin, Janar Abdourahaman Tchiani, ya yi jawabi ta kafafen yada labaran gwamnati a ranar Lahadi, domin bitar halin da ake ciki a kasar a tsawon wadanan gwamman shekaru.

  • Al’ummar Chibok Sun Gudanar Da Bikin Al’adu A Abuja, Sun BuÆ™aci A Mayar Da Su Gidajensu
  • Kasashe 10 Da Bashin IMF Ya Yi Wa Katutu

Yana mai jaddada alwashin samar da mafitar dambarwar da ta biyo bayan juyin mulkin 26 ga watan Yulin 2023.

Batun tsaro na daga cikin muhimman batutuwan da shugaban ya tabo a wannan jawabi da ke zuwa a wani lokacin da Nijar ta yanke hulda a fannin tsaro da tsohuwar kasar mulkin mallaka Faransa, inda ya ce tuni aka fara ganin haske a fagen daga.

Janar Abdourahamane Tchiani, ya ce “a dalilin nasarorin da dakarun tsaronmu ke samu, al’amuran tsaro sun fara daidaituwa sannu a hankali.”

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

Ya ce “abu na zahiri shi ne yadda wasu ‘yan gudun hijirar cikin gida suka fara koma garuruwansu, haka kuma makarantu kusan 200 sun sake budewa a jihar Tilaberi, bayan da suka kasance rufe a tsawon shekaru kusan biyu sanadiyar matsalolin tsaro, sannan mun dauki matakan samar da tsaro kan hanyar shigo da kayan abinci da magunguna da kuma yadda harakokin yau da kullum suka fara dawowa a yankuna da dama.

A cewarsa, “kafuwar kungiyar AES mataki ne na ci gaban kudirin mayar da Sahel wani yankin zaman lafiya da jin dadin rayuwa.”

A fannin yaki da cin hanci, Janar Abdourahamane Tchiani, ya ce “hukumar COLDEFF na nan kan aiki domin bude bincike kan badakalolin da take da hurumi akan su.”

Yana mai jaddada goyon baya ga mambobin wannan hukuma su yi aiki dangance da rantsuwar da suka yi ta yadda al’umma za ta ba su yarda.

Ya kara nanata alkawalinsa da na takwarorinsa na CNSP da gwamnati cewa, ba za su taba bai wa kowa kariya ba. Sanannen abu ne kamarin da cin hanci ya yi a wannan kasa na daga cikin manyan dalilan da ya sa suka hambarar da gwamnati, in ji shi.

Ya kuma yi amfani da wannan dama don mayar da martani ga wadannan kungiyoyi dangane da sharudan da suka gindaya a baya bayan nan.

Ya ce ba za mu taba amincewa dukkan wani jan rai ba, ba kuma za a kara tsoratar da mu ba ko a shimfida mana wata ka’ida ba. kanmu hade yake domin ceton kasa.

Janar Abdouraamane Tchiani ya sha alwashin yin abubuwan da ke yiwuwa, domin tabbatar da ci gaba samar da tsaro da ayyukan jin dadin rayuwar jama’a da hada kan ‘yan kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Juyin MulkiNijarSamun 'Yancin Kai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kayan Masarufi Sun Sake Tashin Gwauron Zabi A Nijeriya 

Next Post

Guardiola Ya Soki ‘Yan Wasan Manchester City Kan Rashin Kwazo

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

13 hours ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

2 days ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

7 days ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
Guardiola Ya Soki ‘Yan Wasan Manchester City Kan Rashin Kwazo

Guardiola Ya Soki 'Yan Wasan Manchester City Kan Rashin Kwazo

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.