• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar Ta Cika Shekaru 65 Da Samun ‘Yancin Kai

by Sadiq
2 years ago
Nijar

Shugaban gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar, ya jinjina wa al’ummar kasar saboda yadda suka jurewa matsalolin da suka biyo bayan takunkumin kungiyar CEDEAO da UEMOA.

A yayin da a ranar Litinin 18 ga watan Disamba kasar Nijar ke bukukuwan cika shekaru 65 da zama jamhuriya, shugaban gwamnatin mulkin sojin, Janar Abdourahaman Tchiani, ya yi jawabi ta kafafen yada labaran gwamnati a ranar Lahadi, domin bitar halin da ake ciki a kasar a tsawon wadanan gwamman shekaru.

  • Al’ummar Chibok Sun Gudanar Da Bikin Al’adu A Abuja, Sun Buƙaci A Mayar Da Su Gidajensu
  • Kasashe 10 Da Bashin IMF Ya Yi Wa Katutu

Yana mai jaddada alwashin samar da mafitar dambarwar da ta biyo bayan juyin mulkin 26 ga watan Yulin 2023.

Batun tsaro na daga cikin muhimman batutuwan da shugaban ya tabo a wannan jawabi da ke zuwa a wani lokacin da Nijar ta yanke hulda a fannin tsaro da tsohuwar kasar mulkin mallaka Faransa, inda ya ce tuni aka fara ganin haske a fagen daga.

Janar Abdourahamane Tchiani, ya ce “a dalilin nasarorin da dakarun tsaronmu ke samu, al’amuran tsaro sun fara daidaituwa sannu a hankali.”

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Ya ce “abu na zahiri shi ne yadda wasu ‘yan gudun hijirar cikin gida suka fara koma garuruwansu, haka kuma makarantu kusan 200 sun sake budewa a jihar Tilaberi, bayan da suka kasance rufe a tsawon shekaru kusan biyu sanadiyar matsalolin tsaro, sannan mun dauki matakan samar da tsaro kan hanyar shigo da kayan abinci da magunguna da kuma yadda harakokin yau da kullum suka fara dawowa a yankuna da dama.

A cewarsa, “kafuwar kungiyar AES mataki ne na ci gaban kudirin mayar da Sahel wani yankin zaman lafiya da jin dadin rayuwa.”

A fannin yaki da cin hanci, Janar Abdourahamane Tchiani, ya ce “hukumar COLDEFF na nan kan aiki domin bude bincike kan badakalolin da take da hurumi akan su.”

Yana mai jaddada goyon baya ga mambobin wannan hukuma su yi aiki dangance da rantsuwar da suka yi ta yadda al’umma za ta ba su yarda.

Ya kara nanata alkawalinsa da na takwarorinsa na CNSP da gwamnati cewa, ba za su taba bai wa kowa kariya ba. Sanannen abu ne kamarin da cin hanci ya yi a wannan kasa na daga cikin manyan dalilan da ya sa suka hambarar da gwamnati, in ji shi.

Ya kuma yi amfani da wannan dama don mayar da martani ga wadannan kungiyoyi dangane da sharudan da suka gindaya a baya bayan nan.

Ya ce ba za mu taba amincewa dukkan wani jan rai ba, ba kuma za a kara tsoratar da mu ba ko a shimfida mana wata ka’ida ba. kanmu hade yake domin ceton kasa.

Janar Abdouraamane Tchiani ya sha alwashin yin abubuwan da ke yiwuwa, domin tabbatar da ci gaba samar da tsaro da ayyukan jin dadin rayuwar jama’a da hada kan ‘yan kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Kasashen Ketare

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Next Post
Guardiola Ya Soki ‘Yan Wasan Manchester City Kan Rashin Kwazo

Guardiola Ya Soki 'Yan Wasan Manchester City Kan Rashin Kwazo

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.