• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
in Kasashen Ketare
0
Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin sojin Nijar ta bude rajista domin tattarawa tare da adana sunayen wadanda ake zargi a kasar da harkokin ta’addanci, kamar yadda tashar talabijin na kasar RTN Tele Sahel ya ruwaito a jiya.

A wata doka da shugaban sojin kasar Birgediya Janar Abdourahmane Tiani ya sanya wa hannu, ta ce duk wani mutum da ya shiga rajistar, za a kwace kadarorinsa, a hana shi tafiya, sannan za a iya kwace shaidar zama dan kasar Nijar.

  • Turkiyya Da Nijar Na Tattauna Ƙulla Kawancen Soji Da Tattalin Arziki
  • Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

Za a sanya mutum ne idan yana taimakon ta’addanci ko dai shiga ciki ko tsarawa ko kasancewa cikin kungiyar ta’addanci ko aware ko wata kungiya da ke barazana ga zaman lafiyar kasar.

Laifukan da za a duba sun kunshi daukar makami domin yaki da kasar, bayar da bayanan sirri ga kasashen waje, taimakon kasashen waje shigowa kasar da kuma fitar da wasu bayanai ko kalamai da za su iya tayar da zaune tsaye a kasar.

Tun bayan hambarar da Mohamed Bazoum daga mulki ne kasar take fuskantar karuwar harkokin ta’addanci, inda aka fi kai hare-hare a kan sojin kasar, musamman a yankin Tillaberi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

A wani labarin kuma, Rahotanni na cewa akalla sojojin Nijar bakwai ne ake zargin ‘yan bindiga sun kashe a ranar 26 ga watan Agusta bayan wani hari da ake kyautata zaton mayakan al-Kaeda ne suka kai a yankin Tillaberi mai fama da rikici a yammacin Nijar.

Shafin tsaro na taswirorin Afirka ta Yamma ya wallafa a shafinsa na D cewa karin sojoji 10 sun bace bayan faruwar lamarin.

Harin dai ya faru ne da misalin karfe shida na safe agogon kasar, inda wasu da dama daga cikin mayakan kungiyar Katiba Hanifa masu alaka da Jama’at Nasr al-Islam wal Muslimin (JNIM) suka kewaye tare da kai farmaki kan wani sansani na rundunar tsaron Nijar (GNN) a Bouloundjounga da ke Tillaberi.

Wannan wurin yana da kusan kilomita hudu daga Samira mai nisan kilomita 10 daga kan iyaka da Burkina Faso.

A martanin da aka mayar, an gudanar da aikin share fage a yankin, kuma an tura wani jirgi mara matuki domin hana ‘yan bindigar tsallaka kogin Sirba.

Sansanin Bouloundjounga, wanda ke da sojoji kusan 80 na da alhakin kare mahakar zinari da ke kusa da tsaunin Samira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBanditNijarTerrorist
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Tawayen RSF Sun Kashe Mutane 25 A Sudan

Next Post

Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

Related

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
Kasashen Ketare

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

2 hours ago
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Kasashen Ketare

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

1 day ago
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Ketare

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

1 day ago
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

2 days ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

6 days ago
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
Kasashen Ketare

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

1 week ago
Next Post
Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.