• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
in Kasashen Ketare
0
Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin sojin Nijar ta bude rajista domin tattarawa tare da adana sunayen wadanda ake zargi a kasar da harkokin ta’addanci, kamar yadda tashar talabijin na kasar RTN Tele Sahel ya ruwaito a jiya.

A wata doka da shugaban sojin kasar Birgediya Janar Abdourahmane Tiani ya sanya wa hannu, ta ce duk wani mutum da ya shiga rajistar, za a kwace kadarorinsa, a hana shi tafiya, sannan za a iya kwace shaidar zama dan kasar Nijar.

  • Turkiyya Da Nijar Na Tattauna Ƙulla Kawancen Soji Da Tattalin Arziki
  • Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

Za a sanya mutum ne idan yana taimakon ta’addanci ko dai shiga ciki ko tsarawa ko kasancewa cikin kungiyar ta’addanci ko aware ko wata kungiya da ke barazana ga zaman lafiyar kasar.

Laifukan da za a duba sun kunshi daukar makami domin yaki da kasar, bayar da bayanan sirri ga kasashen waje, taimakon kasashen waje shigowa kasar da kuma fitar da wasu bayanai ko kalamai da za su iya tayar da zaune tsaye a kasar.

Tun bayan hambarar da Mohamed Bazoum daga mulki ne kasar take fuskantar karuwar harkokin ta’addanci, inda aka fi kai hare-hare a kan sojin kasar, musamman a yankin Tillaberi.

Labarai Masu Nasaba

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

A wani labarin kuma, Rahotanni na cewa akalla sojojin Nijar bakwai ne ake zargin ‘yan bindiga sun kashe a ranar 26 ga watan Agusta bayan wani hari da ake kyautata zaton mayakan al-Kaeda ne suka kai a yankin Tillaberi mai fama da rikici a yammacin Nijar.

Shafin tsaro na taswirorin Afirka ta Yamma ya wallafa a shafinsa na D cewa karin sojoji 10 sun bace bayan faruwar lamarin.

Harin dai ya faru ne da misalin karfe shida na safe agogon kasar, inda wasu da dama daga cikin mayakan kungiyar Katiba Hanifa masu alaka da Jama’at Nasr al-Islam wal Muslimin (JNIM) suka kewaye tare da kai farmaki kan wani sansani na rundunar tsaron Nijar (GNN) a Bouloundjounga da ke Tillaberi.

Wannan wurin yana da kusan kilomita hudu daga Samira mai nisan kilomita 10 daga kan iyaka da Burkina Faso.

A martanin da aka mayar, an gudanar da aikin share fage a yankin, kuma an tura wani jirgi mara matuki domin hana ‘yan bindigar tsallaka kogin Sirba.

Sansanin Bouloundjounga, wanda ke da sojoji kusan 80 na da alhakin kare mahakar zinari da ke kusa da tsaunin Samira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBanditNijarTerrorist
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Tawayen RSF Sun Kashe Mutane 25 A Sudan

Next Post

Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

Related

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
Kasashen Ketare

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

2 days ago
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
Kasashen Ketare

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

1 week ago
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

2 weeks ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

3 weeks ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

3 weeks ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

3 weeks ago
Next Post
Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.