ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Ronaldo

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa yana ganin a kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr ta kasar Saudiyya zai yi ritaya daga buga kwallo a duniya baki daya. A ranar 30 ga watan Disamban 2022 ne kyaftin din tawagar kasar Portugal.

din, Cristiano Ronaldo ya koma buga wasa a kungiyar Al-Nassr ta Saudiyya kuma ya koma kungiyar ne a kan farashin Fam miliyan 200 duk shekara, wanda shi ne albashi mafi tsoka a kwallon kafa.

  • Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0
  • Ronaldo Ya Fashe Da Kuka Bayan Rashin Nasara A Wasan Ƙarshe

Sai dai tun bayan komawarsa Saudiya masu sharhi a kan harkar suke ci gaba da tattauna nasarar da ya samu da akasin haka inda a ranar Asabar ne 17 ga Agusta ce Al-Hilal ta lallasa Al-Nassr da ci hudu da 1 a wasan Saudi Super Cup.

ADVERTISEMENT

Ronaldo ne ya fara zuwa kwallo a wasan bayan minti 44, inda magoya bayan kungiyar suka fara murna, kafin daga bisa murnar ta koma ciki kuma hakan na zuwa ne bayan a ranar 1 ga Yuni, Al-Hilal din ta doke Al-Nassr a wasan Kofin Kings Cup, inda Al-Hilal ta yi nasara a bugun fanareti bayan an tashi canjaras.

Bayan an tashi wasan ne fitaccen dan wasan ya fashe da kuka, inda abokan wasansa suka taru a kansa suna ba shi hakuri haka kuma na biyu Al-Nassr ta kare a gasar Sausi Pro League a kakar bara kuma har yanzu kofin da ya ci tun zuwansa kungiyar ita ce Kofin Arab Club ta kakar bara.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Ganin yadda Al-Hilal ke ci gaba da kaka-gida a wasan kwallon Saudiyyar ce ya sa ake ganin shin akwai amfanin da zuwan Ronaldo ya yi wa Al-Nassr?

A bangaren zura kwallaye ba a cewa komai, domin a kakar bara ya kafa tarihin cin kwallaye a gasar, inda ya zura kwallo 35 a kaka daya, inda ya karya tarihin Abderrazak Hamdallah, wanda ya taba zura kwallo 34 a kakar 2028-2019. Zuwa yanzu, dan wasan na zura kwallo 67, ya taimaka an ci kwallo 16 a wasa 73 da ya buga wa kungiyar ta Al-Nassr. Ke nan za a iya cewa a

matakinsa da dan wasa, ya ci kwallaye, kuma ya nuna bajinta, sai dai duk kungiyar da ya buga wa kwallo ya lashe kofi, ciki har da Sporting CP, inda ya faro a Portugal.

Sai dai yadda Al-Nassr din ba ta lashe kofuna sosai, sai wasu ke diga alamar tambaya a kan nasarar da ya samu a kungiyar domin kafin komawarsa Al-Nassr, Ronaldo ya lashe kofuna da dama a kungiyoyin da ya buga wasa, kamar Manchester United, da Real Madrid, inda ya fi lashe kofuna.

Sannan ya lashe kofuna a kungiyar Jubentus, inda ya je kafin ya koma Saudiyya. Babban dalilin da ya sa kungiyar Al-Nassr ta dauki dan wasa Ronaldo shi ne cin kofi sannan zuwansa zai taimaka wajen ganin wasu ‘yan wasan sun shiga kungiyar, kamar yadda daga baya irinsu Sadio Mane da Aled Telles suka bishi kungiyar.

Sai dai kuma kungiyar Al-Hilal tana da matukar tasiri a kwallon kafa a Saudiyya, sannan ta dauki zakakuran ‘yan wasa daga Nahiyar Turai sama da wadanda Al-Nassr ta dauka wanda hakan ya sa take ci gaba da jan zarenta.

Sai dai har yanzu akwai jan aiki a gaban kungiyar Al-Nassr wajen ganin ta sha gaban kungiyar Al-Hilal musamman lashe kofunan kasar Saudiyya tare kuma da mamaye gasar kasar Saudiyya kamar yadda Al-Hilar ta yi.

Ronaldo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra'ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.