ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Ronaldo

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa yana ganin a kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr ta kasar Saudiyya zai yi ritaya daga buga kwallo a duniya baki daya. A ranar 30 ga watan Disamban 2022 ne kyaftin din tawagar kasar Portugal.

din, Cristiano Ronaldo ya koma buga wasa a kungiyar Al-Nassr ta Saudiyya kuma ya koma kungiyar ne a kan farashin Fam miliyan 200 duk shekara, wanda shi ne albashi mafi tsoka a kwallon kafa.

  • Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0
  • Ronaldo Ya Fashe Da Kuka Bayan Rashin Nasara A Wasan Ƙarshe

Sai dai tun bayan komawarsa Saudiya masu sharhi a kan harkar suke ci gaba da tattauna nasarar da ya samu da akasin haka inda a ranar Asabar ne 17 ga Agusta ce Al-Hilal ta lallasa Al-Nassr da ci hudu da 1 a wasan Saudi Super Cup.

ADVERTISEMENT

Ronaldo ne ya fara zuwa kwallo a wasan bayan minti 44, inda magoya bayan kungiyar suka fara murna, kafin daga bisa murnar ta koma ciki kuma hakan na zuwa ne bayan a ranar 1 ga Yuni, Al-Hilal din ta doke Al-Nassr a wasan Kofin Kings Cup, inda Al-Hilal ta yi nasara a bugun fanareti bayan an tashi canjaras.

Bayan an tashi wasan ne fitaccen dan wasan ya fashe da kuka, inda abokan wasansa suka taru a kansa suna ba shi hakuri haka kuma na biyu Al-Nassr ta kare a gasar Sausi Pro League a kakar bara kuma har yanzu kofin da ya ci tun zuwansa kungiyar ita ce Kofin Arab Club ta kakar bara.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Ganin yadda Al-Hilal ke ci gaba da kaka-gida a wasan kwallon Saudiyyar ce ya sa ake ganin shin akwai amfanin da zuwan Ronaldo ya yi wa Al-Nassr?

A bangaren zura kwallaye ba a cewa komai, domin a kakar bara ya kafa tarihin cin kwallaye a gasar, inda ya zura kwallo 35 a kaka daya, inda ya karya tarihin Abderrazak Hamdallah, wanda ya taba zura kwallo 34 a kakar 2028-2019. Zuwa yanzu, dan wasan na zura kwallo 67, ya taimaka an ci kwallo 16 a wasa 73 da ya buga wa kungiyar ta Al-Nassr. Ke nan za a iya cewa a

matakinsa da dan wasa, ya ci kwallaye, kuma ya nuna bajinta, sai dai duk kungiyar da ya buga wa kwallo ya lashe kofi, ciki har da Sporting CP, inda ya faro a Portugal.

Sai dai yadda Al-Nassr din ba ta lashe kofuna sosai, sai wasu ke diga alamar tambaya a kan nasarar da ya samu a kungiyar domin kafin komawarsa Al-Nassr, Ronaldo ya lashe kofuna da dama a kungiyoyin da ya buga wasa, kamar Manchester United, da Real Madrid, inda ya fi lashe kofuna.

Sannan ya lashe kofuna a kungiyar Jubentus, inda ya je kafin ya koma Saudiyya. Babban dalilin da ya sa kungiyar Al-Nassr ta dauki dan wasa Ronaldo shi ne cin kofi sannan zuwansa zai taimaka wajen ganin wasu ‘yan wasan sun shiga kungiyar, kamar yadda daga baya irinsu Sadio Mane da Aled Telles suka bishi kungiyar.

Sai dai kuma kungiyar Al-Hilal tana da matukar tasiri a kwallon kafa a Saudiyya, sannan ta dauki zakakuran ‘yan wasa daga Nahiyar Turai sama da wadanda Al-Nassr ta dauka wanda hakan ya sa take ci gaba da jan zarenta.

Sai dai har yanzu akwai jan aiki a gaban kungiyar Al-Nassr wajen ganin ta sha gaban kungiyar Al-Hilal musamman lashe kofunan kasar Saudiyya tare kuma da mamaye gasar kasar Saudiyya kamar yadda Al-Hilar ta yi.

Ronaldo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra'ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.