• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ce Ta Fi Tsadar Tafiyar Da Gwamnati A Afirka -RMAFC

by Shehu Yahaya
12 months ago
Nijeriya

Hukumar raba kudaden shiga da hada-hadar kudi ta Nijeriya (RMAFC) ta koka kan tsadar harkokin mulki a Nijeriya tsawon shekaru, tana mai cewa Nijeriya ce mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka tafi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnata.

Hukumar ta ce lamarin da ke da ban tsoro da rashin dorewa kan yadda jama’a ke nuna damuwa da tattaunawa saboda mummunan tasirinsa da ke janyo wa bangaren zuba jari, fadada masana’antu da samar da ababen more rayuwa, da kuma ci gaban hakikanin fannin tattalin arziki.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Naɗa Manjo Janar Olufemi Muƙaddashin Babban Hafsan Sojin Ƙasa

Shugaban hukumar, Dakta Muhammad Bello, shi ne ya bayyana haka a Abuja, inda ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa umarnin da ya bayar na rage yawan ayarin ministoci da manyan jami’an gwamnatinsa a matsayin hanyar rage tsadar tafiyar da gwamnati, yayin da ya bukaci gwamnatocin jihohi su ma su yi koyi da shi.

Ya yi kira da a rage yawan masu rike da mukaman siyasa kamar yadda aka ba da shawarar a cikin kunshin biyan albashi na RMAFC, na masu rike da mukaman siyasa da na gwamnati da kuma tabbatar da yadda ake kashe kudaden gwamnati a kowane mataki.

Shugaban RMAFC ya ce, “Shaidu sun nuna cewa Nijeriya ce kasa wacce aka fi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnati a duk kasashen da suke Afirka. Hukumar ta fito fili ta bayyana matsayarta kan wannan batu ta hanyar gabatar da takarda.

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“A bayyane yake cewa farashin mulkin Nijeriya yana daya daga cikin mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka, wanda ya kawo cikas ga gwamnati wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta kamar su raya ababen more rayuwa, samar da ingantaccen kiwon lafiya, inganta harkokin ilimi da dai sauransu.”

Dakta Shehu ya ce matakin zai taimaka matuka wajen rage tsadar harkokin mulki, wanda wani bangare ne ke da alhakkin rage samar da ababen more rayuwa da walwala da faduwar zuba jari da rashin aikin yi da karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Ya kara da cewa babu wata al’umma da za ta iya samun ci gaba mai ma’ana, sai dai idan ta samar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’amura gwamnati da za su iya amfani da albarkatun kasa domin amfanin kowa.

Ya ce hukumar RMAFC ta yi shekaru da yawa tana yaki da lamarin, ba wai kawai ta bayar da shawarar rage farashin mulki ba ne a matsayin hanyar tadanar kudade, sannan kuma ta ba da shawarwari masu yawa ga gwamnati a dukkan matakai kan tsarin bukatar rage yawan kashe kudin da ba dole ba da kuma lura da kashe kudi kan ayyukan ci gaba wadanda za su yi tasiri mai kyau ga rayuwar ‘yan kasa.

A cewarsa, tsadar harkokin mulki a Nijeriya ya samo asali ne sakamakon tsadar manyan ofisoshi, da yawan ma’aikatun da hukumomin gwamnati da kuma cin hanci da rashawa.

“Sauran abubuwan sun hada da tsadar ayyukan gwamnati sakamakon gazawar ababen more rayuwa, tsadar tsaro sakamakon ta da kayan baya, garkuwa da mutane da ta da kayan baya da kuma fashi da makami, yawan albashi da alawus alawus, almubazzaranci da ayyuka da kashe kudade, dimbin basussuka na gida da waje da kuma raunin cibiyoyin tilasta aiwatarwa da ayyuka,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Labarai

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano
Manyan Labarai

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Next Post
Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

LABARAI MASU NASABA

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

October 26, 2025
Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.