• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ce Ta Fi Tsadar Tafiyar Da Gwamnati A Afirka -RMAFC

by Shehu Yahaya
10 months ago
in Labarai
0
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar raba kudaden shiga da hada-hadar kudi ta Nijeriya (RMAFC) ta koka kan tsadar harkokin mulki a Nijeriya tsawon shekaru, tana mai cewa Nijeriya ce mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka tafi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnata.

Hukumar ta ce lamarin da ke da ban tsoro da rashin dorewa kan yadda jama’a ke nuna damuwa da tattaunawa saboda mummunan tasirinsa da ke janyo wa bangaren zuba jari, fadada masana’antu da samar da ababen more rayuwa, da kuma ci gaban hakikanin fannin tattalin arziki.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Manjo Janar Olufemi MuÆ™addashin Babban Hafsan Sojin Ƙasa

Shugaban hukumar, Dakta Muhammad Bello, shi ne ya bayyana haka a Abuja, inda ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa umarnin da ya bayar na rage yawan ayarin ministoci da manyan jami’an gwamnatinsa a matsayin hanyar rage tsadar tafiyar da gwamnati, yayin da ya bukaci gwamnatocin jihohi su ma su yi koyi da shi.

Ya yi kira da a rage yawan masu rike da mukaman siyasa kamar yadda aka ba da shawarar a cikin kunshin biyan albashi na RMAFC, na masu rike da mukaman siyasa da na gwamnati da kuma tabbatar da yadda ake kashe kudaden gwamnati a kowane mataki.

Shugaban RMAFC ya ce, “Shaidu sun nuna cewa Nijeriya ce kasa wacce aka fi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnati a duk kasashen da suke Afirka. Hukumar ta fito fili ta bayyana matsayarta kan wannan batu ta hanyar gabatar da takarda.

Labarai Masu Nasaba

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

“A bayyane yake cewa farashin mulkin Nijeriya yana daya daga cikin mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka, wanda ya kawo cikas ga gwamnati wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta kamar su raya ababen more rayuwa, samar da ingantaccen kiwon lafiya, inganta harkokin ilimi da dai sauransu.”

Dakta Shehu ya ce matakin zai taimaka matuka wajen rage tsadar harkokin mulki, wanda wani bangare ne ke da alhakkin rage samar da ababen more rayuwa da walwala da faduwar zuba jari da rashin aikin yi da karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Ya kara da cewa babu wata al’umma da za ta iya samun ci gaba mai ma’ana, sai dai idan ta samar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’amura gwamnati da za su iya amfani da albarkatun kasa domin amfanin kowa.

Ya ce hukumar RMAFC ta yi shekaru da yawa tana yaki da lamarin, ba wai kawai ta bayar da shawarar rage farashin mulki ba ne a matsayin hanyar tadanar kudade, sannan kuma ta ba da shawarwari masu yawa ga gwamnati a dukkan matakai kan tsarin bukatar rage yawan kashe kudin da ba dole ba da kuma lura da kashe kudi kan ayyukan ci gaba wadanda za su yi tasiri mai kyau ga rayuwar ‘yan kasa.

A cewarsa, tsadar harkokin mulki a Nijeriya ya samo asali ne sakamakon tsadar manyan ofisoshi, da yawan ma’aikatun da hukumomin gwamnati da kuma cin hanci da rashawa.

“Sauran abubuwan sun hada da tsadar ayyukan gwamnati sakamakon gazawar ababen more rayuwa, tsadar tsaro sakamakon ta da kayan baya, garkuwa da mutane da ta da kayan baya da kuma fashi da makami, yawan albashi da alawus alawus, almubazzaranci da ayyuka da kashe kudade, dimbin basussuka na gida da waje da kuma raunin cibiyoyin tilasta aiwatarwa da ayyuka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaNijeriyaTsadar Raywa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fito Da Sabbin  Nau’in Kaji 2 Da Iri

Next Post

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Related

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

3 hours ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

6 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

7 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

9 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

10 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

13 hours ago
Next Post
Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

LABARAI MASU NASABA

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya FarfaÉ—o Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya FarfaÉ—o Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.