ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ce Ta Fi Tsadar Tafiyar Da Gwamnati A Afirka -RMAFC

by Shehu Yahaya
2 years ago
Nijeriya

Hukumar raba kudaden shiga da hada-hadar kudi ta Nijeriya (RMAFC) ta koka kan tsadar harkokin mulki a Nijeriya tsawon shekaru, tana mai cewa Nijeriya ce mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka tafi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnata.

Hukumar ta ce lamarin da ke da ban tsoro da rashin dorewa kan yadda jama’a ke nuna damuwa da tattaunawa saboda mummunan tasirinsa da ke janyo wa bangaren zuba jari, fadada masana’antu da samar da ababen more rayuwa, da kuma ci gaban hakikanin fannin tattalin arziki.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Naɗa Manjo Janar Olufemi Muƙaddashin Babban Hafsan Sojin Ƙasa

Shugaban hukumar, Dakta Muhammad Bello, shi ne ya bayyana haka a Abuja, inda ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa umarnin da ya bayar na rage yawan ayarin ministoci da manyan jami’an gwamnatinsa a matsayin hanyar rage tsadar tafiyar da gwamnati, yayin da ya bukaci gwamnatocin jihohi su ma su yi koyi da shi.

ADVERTISEMENT

Ya yi kira da a rage yawan masu rike da mukaman siyasa kamar yadda aka ba da shawarar a cikin kunshin biyan albashi na RMAFC, na masu rike da mukaman siyasa da na gwamnati da kuma tabbatar da yadda ake kashe kudaden gwamnati a kowane mataki.

Shugaban RMAFC ya ce, “Shaidu sun nuna cewa Nijeriya ce kasa wacce aka fi kashe kudade wajen tafiyar da gwamnati a duk kasashen da suke Afirka. Hukumar ta fito fili ta bayyana matsayarta kan wannan batu ta hanyar gabatar da takarda.

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

“A bayyane yake cewa farashin mulkin Nijeriya yana daya daga cikin mafi girma a yankin kudu da hamadar Saharan Afirka, wanda ya kawo cikas ga gwamnati wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta kamar su raya ababen more rayuwa, samar da ingantaccen kiwon lafiya, inganta harkokin ilimi da dai sauransu.”

Dakta Shehu ya ce matakin zai taimaka matuka wajen rage tsadar harkokin mulki, wanda wani bangare ne ke da alhakkin rage samar da ababen more rayuwa da walwala da faduwar zuba jari da rashin aikin yi da karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Ya kara da cewa babu wata al’umma da za ta iya samun ci gaba mai ma’ana, sai dai idan ta samar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’amura gwamnati da za su iya amfani da albarkatun kasa domin amfanin kowa.

Ya ce hukumar RMAFC ta yi shekaru da yawa tana yaki da lamarin, ba wai kawai ta bayar da shawarar rage farashin mulki ba ne a matsayin hanyar tadanar kudade, sannan kuma ta ba da shawarwari masu yawa ga gwamnati a dukkan matakai kan tsarin bukatar rage yawan kashe kudin da ba dole ba da kuma lura da kashe kudi kan ayyukan ci gaba wadanda za su yi tasiri mai kyau ga rayuwar ‘yan kasa.

A cewarsa, tsadar harkokin mulki a Nijeriya ya samo asali ne sakamakon tsadar manyan ofisoshi, da yawan ma’aikatun da hukumomin gwamnati da kuma cin hanci da rashawa.

“Sauran abubuwan sun hada da tsadar ayyukan gwamnati sakamakon gazawar ababen more rayuwa, tsadar tsaro sakamakon ta da kayan baya, garkuwa da mutane da ta da kayan baya da kuma fashi da makami, yawan albashi da alawus alawus, almubazzaranci da ayyuka da kashe kudade, dimbin basussuka na gida da waje da kuma raunin cibiyoyin tilasta aiwatarwa da ayyuka,” in ji shi.

Nijeriya
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin
Labarai

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Labarai

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Next Post
Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

LABARAI MASU NASABA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026
Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.