• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Jerin Ƙasashen Da Cin Hanci Da Rashawa Suka Yi Wa Katutu A 2024 -Rahoto

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
in Labarai
0
Nijeriya Na Jerin Ƙasashen Da Cin Hanci Da Rashawa Suka Yi Wa Katutu A 2024 -Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar Transparency Internaltional ta fitar da rahotonta na ayyukan cin hanci da rashawa a duniya cikin shekara ta 2024, wato Corruption Perception Inded.

Rahoton ya yi nazari ne kan ƙasashe 180 bisa la’akari da hujjojin masana da kuma ‘yan kasuwa kan matsalar rashawa na kowace kasa

  • Thomas Bach Ya Bai Wa Cmg Izinin Sarrafa Watsa Labarun Gasar Olympics Ta Lokacin Hunturu Ta Milan Ta 2026
  • Fatara Da Talauci Na Yi Wa ‘Yan Nijeriya Miliyan 13 Barazanar Fadawa Kangin Talauci A 2025 — Rahoto

Haka nan rahoton ya dogara da majiyoyi 13 masu zaman kansu domin dora kasashen kan mizani daga sifili zuwa 100; sifili na nufin matsalar rashawa ta yi muni sosai yayin da 100 ke nufin babu matsalar baki daya.

Rahoton ya kara fito da bambancin da ke tsakanin kasashen da ke bin tafarkin dimokuradiyya da kuma wadanda ke bin tsari na kama-karya.

Lamarin ya nuna cewa kasashen da ke bin tafarkin dimokuradiyya sau da kafa na da matsakaicin maki da ya kai 73, wadanda ke bin tsarin dimokuradiyya mai cike da kurakurai kuma na da matakaicin maki 47 sai kuma kasashen da ba su bin tafarkin dimokuradiyya wadanda ke da matsakaicin maki 33.

Labarai Masu Nasaba

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ƙasashen da suke da saukin cin hanci a duniya

Mafi yawan kasashen da rahoton ya nuna cewa babu yawaitar matsalar cin hanci da rashawa suna a nahiyar Turai ne.

Bakwai daga cikin kasashen 10 na farko, wadanda ba su da matsalar Rasha duk a yankin Tarayyar ta Turai suke.

Qasar da ta fi kowace a duniya samun maki a bangaren yaki da rashawa ita ce Denmark, wadda take da maki 90.

Sai kuma Finland mai maki 88, ta uku kuma ita ce Singapore, wadda ke a kudu maso gabashin nahiyar Asiya.

Ga yadda kasashen 10 na farko suka kasance:

1. Denmark – Maki 90

2. Finland – Maki 88

3. Singapore – Maki 84.

4. New Zealand – Maki 83.

5. Ludembourg – Maki 81.

6. Norway – Maki 81.

7. Swtizerland – Maki 81

8. Sweden – Maki 80.-

9. Netherlands – Maki 78-

10. Austria – Maki 77.

Sai dai rahoton na Tranparency International ya ce duk da cewa kasashen Turai su ne suka fi samun yabo a rahoton, to amma makin da suke samu ya ragu cikin shekara biyu a jere.

Rahoton ya ce wasu shugabannin kasashen na Turai sun mayar da hankali wajen “abin da zai dadada wa harkar kasuwanci kawai a maimakon abubuwan da za su inganta rayuwar al’umma”.

Ƙasashen da ke kurar-baya

Rahoton ya nuna cewa akasarin kasashen da ke kasan jadawalin suna a nahiyar Afirka ne, inda nahiyar ke da kasashe shida cikin 10 da suka samu maki mafi karanci.

Sauran kasashen sun fito ne daga nahiyar Amurka ta kudu sai kuma Gabas ta takiya.

Sudan ta Kudu da Somaliya su ne kasashen da ke kasan tebur, inda Sudan ta Kudu ke da maki 8 kacal yayin da Somaliya ke da maki 9.

170. Sudan – Maki 15 –

172. Nicaragua – Maki 14-

173. Ekuatorial Guinea – Maki 13

173. Eritriya – Maki 13-

173. Libya – Maki 13-

173.Yemen – Maki 177. Syriya – Maki 12 –

178. Venezuela – Maki 10-

179. Somaliya – Maki 9-

180. Sudan ta Kudu – Maki 8

Rahoton ya ce nahiyar Afirka, kudu da hamadar sahara ce ta samu maki mafi karanci. Hakan ya faru ne sanadiyyar rikice-rikice masu alaka da sauyin yanayi wadanda ke tarnaki ga ci gaban yankin.

Sai dai rahoton ya ce bunkasar yaki da rashawa a Gabas ta Tsakiya da Arewacin Amurka wani abu ne na farin ciki, sai dai wannan ne karo na farko da aka samu haka a cikin shekara 10, kuma ci gaban da maki daya ne kacal.

Mene ne matsayin Nijeriya da Nijar da Ghana?

A tsakanin Nijeriya da Nijar da Ghana, Ghana ce ta fi tabuka abin kirki, inda take a matsayi na 80 bayan samun maki 40.

Sai Jamhuriyar Nijar, wadda take a matsayi na 107 bayan samun maki 34.

Nijeriya na a matsayi na 140 inda ta samu maki 26, tare da wasu kasashen kamar Medico da Iraki da Kamaru.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NigeriaRashawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Karon Farko An Zabi Mace Shugabar ALGON A Kano

Next Post

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manyan Jami’an Kasashe Daban Daban

Related

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

1 hour ago
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
Labarai

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

10 hours ago
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja
Labarai

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

11 hours ago
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
Labarai

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

12 hours ago
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
Labarai

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

13 hours ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Labarai

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

14 hours ago
Next Post
Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manyan Jami’an Kasashe Daban Daban

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manyan Jami’an Kasashe Daban Daban

LABARAI MASU NASABA

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.