• English
  • Business News
Tuesday, May 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

by Sadiq
3 weeks ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa biyayyarsa a siyasa tana ga Nijeriya ne, ba ga kowanne mutum ko jam’iyya ba.

El-Rufai ya yi wannan bayani ne yayin ziyarar da ya kai Jihar Kano, inda ya gana da Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, da kuma shugabannin jam’iyyar SDP na jihar.

  • Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Ayyukan Sadarwa
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai

Ya ce dalilin da ya sa ya koma jam’iyyar SDP shi ne domin ya gina wata madaidaiciyar hanya ta siyasa da za ta ceto ƙasar nan.

“Shekaru goma sha biyu da suka wuce, mun kafa jam’iyyar APC kuma muka kayar da shugaban Æ™asa mai ci. Amma yau abubuwa sun canza. Muna haÉ—a kan ‘yan Nijeriya da suka gaji da halin da ake ciki a Æ™arÆ™ashin jam’iyyar SDP, wacce ke da adalci da dimokuraÉ—iyya,” in ji El-Rufai.

Ya kuma ƙara da cewa bai taɓa fifita jam’iyya sama da Nijeriya ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

“Lokacin da abubuwa suka fara lalacewa a lokacin shugaba Buhari, na fito na faÉ—i gaskiya. Lokacin da tsarin sauya fasalin Naira ya jefa jama’a cikin wahala, na Æ™alubalanci gwamnati duk da cewa jam’iyyar APC ce ke kan mulki. Na fi biyayya ga Nijeriya fiye da kowane mutum,” in ji shi.

El-Rufai ya ƙaryata jita-jitar cewa fushinsa da gwamnatin Shugaba Tinubu ne ya sa ya fice daga APC.

Ya ce yana da shekaru 65, kuma babu wani abu da ya rage masa a siyasa da zai nema, sai dai kawai yana jin cewa matsalolin Nijeriya sun yi tsanani sosai wanda ba zai zauna ya yu shiru ba.

“Zan iya yin ritaya cikin kwanciyar hankali, amma Nijeriya na fuskantar babbar barazana. Wannan ba don kaina ba ne – don ceton Æ™asa ne,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa dole a zaɓi shugaban ƙasa mai nagarta da hangen nesa, ba wai kawai din ya fito daga wata jiha ba.

“Matsalolin da muke fuskanta sun fi girman la’akari da inda mutum ya fito. Muna buÆ™atar shugabanni masu hangen nesa da Æ™warewa don gyara Nijeriya,” ya bayyana.

Da yake magana kan sauya sheƙar wasu ‘yan siyasa zuwa APC, El-Rufai ya ce jam’iyyar SDP tana mayar da hankali ne kan gina goyon baya daga jama’a, ba wai kawai neman manyan ‘yan siyasa ba.

“Gwamna É—aya yana da Æ™uri’a É—aya ne kawai. Jama’a ne ke yin zaÉ“e, ba manyan ‘yan siyasa ba,” ya jaddada.

A ƙarshe, El-Rufai ya ce tafiyar SDP tana ci gaba da karɓuwa a dukkanin sassan Nijeriya, ba a yankuna kaɗan kaɗai ba.

“Muna ci gaba da gina goyon baya a faÉ—in Æ™asar nan. Aikin gina Æ™asa yana faruwa ne a tsakanin talakawa, ba kawai a kafafen yaÉ—a labarai ba,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCEl-RufaikanoPDPSDPZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo

Next Post

Gwamnan Bauchi Ya NaÉ—a Sabbin Hadimai 173

Related

Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

57 minutes ago
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da É—umi-É—uminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

2 hours ago
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 

2 hours ago
Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya
Manyan Labarai

Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON

6 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22

7 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara

21 hours ago
Next Post
Gwamnan Bauchi Ya NaÉ—a Sabbin Hadimai 173

Gwamnan Bauchi Ya NaÉ—a Sabbin Hadimai 173

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

May 20, 2025
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

May 20, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 

May 20, 2025
NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali

NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali

May 20, 2025
Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama

Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama

May 20, 2025
Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci

Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa

May 20, 2025
Xi Jinping Ya Ziyarci Birnin Luoyang Na Lardin Henan

Xi Jinping Ya Ziyarci Birnin Luoyang Na Lardin Henan

May 20, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum Sanye Da Kayan Mata A Coci A Adamawa

May 20, 2025
Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON

May 20, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22

Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22

May 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.