Hukumar hasashen yanayi ta Nijeriya a hasashen da ta fitar a karshen mako a Abuja, ta yi hasashen za a yi tsawa tare da ruwan sama daga ranar Asabar zuwa Litinin a fadin Nijeriya.
Ta ce da sanyin safiya ana sa ran za a yi tsawa a sassan jihohin Taraba, Kebbi, Zamfara, Kaduna da Adamawa a yankin Arewa.
Ana sa ran za a yi ruwan sama a wasu sassan jihohin Kebbi, Taraba, Zamfara, Borno, Kaduna, Sokoto, Gombe, da Bauchi.
“A yankin Arewa ta Tsakiya, ana sa ran za a yi tsawa da sanyin safiya a sassan jihohin Benuwe, Filato, Neja, Babban Birnin Tarayya, da Jihar Nasarawa.
“A washegari, ana hasashen tsawa da ruwan sama a wasu sassan babban birnin tarayya, Neja, Nasarawa, Benuwe, Kwara, Kogi, da Filato.
“A yankin Kudu, ana sa ran samun hadari tare da yiwuwar samun ruwan sama a sassan jihohin Enugu, Ebonyi, Cross River, Legas, Akwa Ibom, Ribas, da Bayelsa,” in ji NiMet.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp