• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Horar Da Jami’anta Na Hulɗa Da Jama’a Kan Dabarun Aiki Na Zamani

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
NIS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta shirya taron bita na kwanaki biyu ga jami’anta da ke aiki a sashin hulɗa da jama’a a faɗin ƙasar nan kan dabarun sadarwa game da yaƙi da shige da fice ba bisa ƙa’ida ba.

Taron bitar ya gudana ne tare da haɗin gwiwar gidauniyar ‘Konrad Adenauer Foundation’, wanda aka yi a otel ɗin Fraser Suites da ke Abuja, da ya samu halartar dukkan masu magana da yawun hukumar ta NIS.

Da yake gabatar da jawabi lokacin buɗe taron, shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris ya bayyana farin cikinsa game da muhimmanci samun horo ga masu magana da yawun hukumar.

CGI Isah Jere, wanda ya samu wakilcin ACG AM Usman ya ce wannan bitar zai ƙara himma da ƙwazon jami’an wajen daƙile shige da fice ba bisa ƙa’ida ba, musamman ma fasa ƙwaurin shige da fice.

  • Doka Za Ta Yi Aiki Kan Dan Chanan Da Ya Kashe Ummita – Ganduje

Shugaban hukumar ya yaba wa gidauniyar bisa wannan gagarumar ƙoƙari wajen inganta aikin hukumar. Yana mai cewar sakamakon bitar zai zama an samu ruɓanya harkokin sadarwar hukumar wajen faɗakar da al’umma kan yaƙi da dukkan ayyukan shige da fice waɗanda ba sa kan ƙa’ida a ɗaukacin iyakokin ƙasar nan.

Labarai Masu Nasaba

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Ya ƙara da cewa hukumarsa ta ɗauki wasu dabaru wajen yaƙi da fasa ƙwaurin shige da fice waɗanda suke daidai da na Majalisar Ɗinkin Duniya kamar yadda dokar hukumar ta shekarar 2015 ta tanada.

A cewarsa, wannan bita ta zo a kan gaɓa domin za ta ƙara ƙoƙarin hukumar wajen ɗaukan matakai dangane da sha’anin harkokin shige da fice da ba sa kan tsari.

Ya buƙaci dukkan jami’an da suka amfana da shirin su yi ƙoƙarin yin amfani da abubuwan da suka koya daga wannan taron.

NIS

Tun da farko da yake jawabi, Daraktan Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), Dakta Tony Luka Elumelu ya bayyana cewa taron bitar yana da matuƙar muhimmanci ga hukumar NIS.

Ya ce a matsayinsa na tsohon ma’aikacin hukumar NIS idan aka ambaci hukumar, dole yana da abubuwan faɗi game da ƙwazon shugabanni da jami’anta.

Daraktan ya ce idan ana buƙatar hukumar NIS ta isar wa ‘yan Nijeriya sahihin saƙo, to dole a ɗauki matakin horar da masu magana da da yawunta da ke faɗin ƙasar nan.

Ya ƙara da cewa ta hanyar bai wa jami’an horo ne za a samu damar tace bayanai masu inganci ta yadda za a isar wa ‘yan Nijeriya. Ya ce bitar za ta taimaka wajen toshe ɓarna mai yawa, musamman harkokin shige da fice ba bisa ƙa’ida ba.

Ya nunar da cewa ta hanyar samun horo ne hukumar ta ciri tuta a tsakanin takwarorinta na ƙasar nan, musamman yadda ta sauya daga tsohon yayi ta koma na zamani inda hakan ya sauƙaƙa ayyukan hukumar.

Da yake zantawa da wakilin LEADERSHIP Hausa, ɗaya daga cikin waɗanda suka amfana da bitar wanda ya kasance mai magana da yawun hukumar NIS a Jihar Adamawa, Yawuba Muhammed ya bayyana cewa taron bitar zai ƙara bunƙasa harkokin ayyukan hukumar gaba ɗaya, musamman a iyakar Nijeriya da Kamaru. Kamar yadda ya ce, lallai wannan bita za ta taimaka wajen daƙile kwararowar baƙin haure a iyakan Nijeriya da Kamaru.

A cewarsa, ɗaya daga cikin muhummancin wannan bita shi ne, samun dabarun sadarwa domin sanar da cikakken sahihin rahoto ga mutane a zamanance.

Ita ma da take tofa albarkacin bakinta ga LEADERSHIP Hausa, jami’ar hulɗa da jama’a ta NIS a Jihar Bayelsa, ED Itimitula Ideinmo- Cokkey ta bayyana cewa bitar za ta ƙara musu himma wajen gabatar da bayanai, musamman kan yaƙi da shige da fice ba bisa ƙa’ida ba.

Ta ce kowanni jami’in hukumar yana da matuƙar muhimmanci ya samu irin wannan horo domin samun faɗakarwa mai inganci.

  • https://leadership.ng/nis-unodc-unveil-report-on-migrants-smuggling/

Gobe Talata ake sa ran kammala taron bitar jami’an na NIS a vangaren hulda da jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Da Takwaransa Na Togo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

Next Post

Adadin Jarin Waje Da Sin Ta Samu A Watanni 8 Na Farkon Bana Ya Kai Yuan Biliyan 892.74

Related

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

16 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

16 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

16 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

18 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

19 hours ago
Next Post
Adadin Jarin Waje Da Sin Ta Samu A Watanni 8 Na Farkon Bana Ya Kai Yuan Biliyan 892.74

Adadin Jarin Waje Da Sin Ta Samu A Watanni 8 Na Farkon Bana Ya Kai Yuan Biliyan 892.74

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.