• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Raba Ruwan Sha Ga ‘Yan Gudun Hijira A Yenagoa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Bayelsa Ta Raba Ruwan Sha Ga ‘Yan Gudun Hijira A Yenagoa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturola Janar na hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS), Isa Jere Idris ya umarci kwanturolan hukumar reshen jihar Bayelsa, James Sunday da ya ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira tare da samar musu da tallafin ruwan sha domin tabbatar da suna shan ruwa mai tsafta kuma mai inganci ga yara da manya.

  • NIS Ta Murza Gashin Baki, Ta Kori Jami’ai 8, Ta Ladabtar Da Wasu Da Dama

Umarnin kai tsaftacaccen ruwan shan ya shafi sansanin ‘yan gudun hijira ta OX- BOW da ke Lake inda gwamnatin jihar Bayelsa ta ajiye dubban ‘yan gudun hijira da iyalansu a wajen a matsayin wurin zama na wucin gadi.

A wata sanarwar da sashin yada labarai na NIS reshen Bayelsa ya fitar wa manema labarai ta nuna cewa, wannan karamcin na shugaban hukumar na zuwa ne sakamakon ambaliyar ruwan sama da aka samu wanda ya yi wa iyalai da gidaje daban-daban barna.

Kazalika, kwanturolan hukumar ya kuma mika sakon fatan alkairisa ga jami’ansa da ke aiki a Bayelsa da su ma ambaliyar ta shafa, kana ya umarci cewa kwamiti mai karfi daga shalkwatar hukumar ya ziyarci jami’ai su 64 da ambaliyar ta shafa tare da taya su alhini gami da shi shawarar abubuwan da suka dace.

Kwanturolan hukumar ta Immigration reshen jihar Bayelsa, James Sunday ya gode tare da yaba wa shugabansu bisa umarnin da ya bayar domin nuna tausayawa da jin kan wadanda lamarin ya shafa na ambaliyar ruwa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

James ya ce cikin taimakon Allah sun samu nasarar taskace muhimman takardu da bayanan hukumar kafin lokacin da ambaliyar ya zo ya yi barna a cikin shalkwatar hukumar da ke Bayelsa kuma yanzu haka ofishin hukumar na gudanar da aikace-aikacensa a sabon muhalli da ke kusa da Yenagoa kafin lokacin da za a gyara muhallin nasu domin su koma su cigaba da gudanar da aiki a ciki.

Har ila yau, sanarwar ta yi amfani da wannan damar wajen gargadin jami’an hukumar ta NIS da kada suke barin wajajen aikinsu a AWOL ko wani wajen domin kauce wa fushin hukumar da ka iya kaiwa a hukunta jami’i ko jami’a ko ma kora daga aiki gaba daya, “Za a ci gaba da sanya ido da bibiyar ayyukan jami’ai, duk ma’aikacin da aka samu da barin wajen aiki zai fuskanci hukunci,” in ji sanarwar.

  • https://leadership.ng/nis-says-64-personnel-displaced-as-flood-submerges-bayelsa-office/

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Dalilin Da Ya Sa Aka Kara Samun Sabbin Kayayyaki Da Fasahohi A Wajen Bikin CIIE?

Next Post

APC Ta Naɗa Kannywood Cikin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu/Shettima

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

1 hour ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

4 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

5 hours ago
NIS
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

6 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

8 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

8 hours ago
Next Post
APC Ta Naɗa Kannywood Cikin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu/Shettima

APC Ta Naɗa Kannywood Cikin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu/Shettima

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
NIS

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.