ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Murza Gashin Baki, Ta Kori Jami’ai 8, Ta Ladabtar Da Wasu Da Dama

by Sulaiman
4 years ago
NIS

Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta kasa NIS, CGI Isah Jere Idris MFR ya sanar da korar wasu jami’an hukumar su takwas (8) daga bakin aiki tare da hukunta wasu jami’an 18 da aka samu da aikata laifuka daban-daban da ya saba wa dokar hukumar don ladabtarwa.

Sanarwar ta biyo bayan amincewar Hukumar Gudanarwar Rundunonin da ke karkashin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB) wadda a njna cewa munanan ayyukan jami’an sun kasance abin da ma’aikatar ba za ta amince a ce jami’anta ne ke aikata irin wannan halayya ba.

In za a iya tunawa, jami’ai 35 ne ake tuhumarsu a wannan shekara, wadanda aka gabatar a gaban babban kwamitin ladabtarwa (SDC) da kuma na tabbatar da bin tsarin aiki (ORT) don tabbatar da tuhume-tuhume daban-daban na laifuffukan da suka shafi ladabtarwa wanda ake zarginsu da aikatawa, wadanda suka hada da cin zarafi abokan huldarsu, ayyukan Allah wadai, rashin gaskiya, barin wurin aiki ba tare da izinin hukumar ba (AWOL) da sauransu.

ADVERTISEMENT

Bayan kammala binciken da kwamitocin suka yi, SDC da ORT, an kori jami’ai takwas da suka hada da Babban Sufiritanda na Shige da Fice (CSI), mataimakan Sufiritantanda na Shige da Fice (DSI) biyu, mataimakan Sufiritande na Shige da Fice II (ASI2) da kuma wasu Uku masu kananan mukami.

Bugu da kari, an umurci wani Babban Sufiritanda na Shige da Fice da ya yi takardar ritayar dole yayin da wasu jami’ai tara (9) aka rage musu mukami. Sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) wanda aka maida zuwa matsayin Sufeto na Shige da Fice; da Sufeto biyu da aka maida zuwa mukamin Mataimakin Sufeto; da wasu masu kananan mukamai su shida (6) da aka kwace mukamin da suke kai.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Sannan kuma, akwai wasu Jami’ai tara (9) da aka raba wa takardar gargadi, sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) da Kananan Ma’aikata takwas (8), sannan kwamitocin sun wanke wasu jami’ai shida (6) daga dukkan zarge-zargen da ake yi musu.

Bugu da kari, Kwanturola Janar din ya amince da sauya wa jami’ai 100 da aka tura filin jirgin sama na Legas wurin aiki nan take yayin da ya ba da umurnin tuhumar wasu don tabbatar da zargin da ake musu kan badakala a filin jirgin da aka ba da rahoto kwanan nan kana a san matakin da za a dauka akan su.

Kwanturolan Janar, na amfani da wannan damar don tabbatar wa ‘yan kasa da cewa, Hukumar NIS ba za ta lamunta duk wani hali ko nau’i na halin rashin gaskiya ba ga duk Jami’anta, don haka, yana kira ga jama’a da su ci gaba da bada rahoton duk wani nau’in hali na cin zarafi ko rashin gaskiya a bakin aiki da aka ga jami’in hukumar na aikatawa.

NIS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Biyu A Harin Nakiya A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.