ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Murza Gashin Baki, Ta Kori Jami’ai 8, Ta Ladabtar Da Wasu Da Dama

by Sulaiman
4 years ago
NIS

Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta kasa NIS, CGI Isah Jere Idris MFR ya sanar da korar wasu jami’an hukumar su takwas (8) daga bakin aiki tare da hukunta wasu jami’an 18 da aka samu da aikata laifuka daban-daban da ya saba wa dokar hukumar don ladabtarwa.

Sanarwar ta biyo bayan amincewar Hukumar Gudanarwar Rundunonin da ke karkashin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB) wadda a njna cewa munanan ayyukan jami’an sun kasance abin da ma’aikatar ba za ta amince a ce jami’anta ne ke aikata irin wannan halayya ba.

In za a iya tunawa, jami’ai 35 ne ake tuhumarsu a wannan shekara, wadanda aka gabatar a gaban babban kwamitin ladabtarwa (SDC) da kuma na tabbatar da bin tsarin aiki (ORT) don tabbatar da tuhume-tuhume daban-daban na laifuffukan da suka shafi ladabtarwa wanda ake zarginsu da aikatawa, wadanda suka hada da cin zarafi abokan huldarsu, ayyukan Allah wadai, rashin gaskiya, barin wurin aiki ba tare da izinin hukumar ba (AWOL) da sauransu.

ADVERTISEMENT

Bayan kammala binciken da kwamitocin suka yi, SDC da ORT, an kori jami’ai takwas da suka hada da Babban Sufiritanda na Shige da Fice (CSI), mataimakan Sufiritantanda na Shige da Fice (DSI) biyu, mataimakan Sufiritande na Shige da Fice II (ASI2) da kuma wasu Uku masu kananan mukami.

Bugu da kari, an umurci wani Babban Sufiritanda na Shige da Fice da ya yi takardar ritayar dole yayin da wasu jami’ai tara (9) aka rage musu mukami. Sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) wanda aka maida zuwa matsayin Sufeto na Shige da Fice; da Sufeto biyu da aka maida zuwa mukamin Mataimakin Sufeto; da wasu masu kananan mukamai su shida (6) da aka kwace mukamin da suke kai.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Sannan kuma, akwai wasu Jami’ai tara (9) da aka raba wa takardar gargadi, sun hada da Mataimakin Sufiritanda na Shige da Fice II (ASI2) da Kananan Ma’aikata takwas (8), sannan kwamitocin sun wanke wasu jami’ai shida (6) daga dukkan zarge-zargen da ake yi musu.

Bugu da kari, Kwanturola Janar din ya amince da sauya wa jami’ai 100 da aka tura filin jirgin sama na Legas wurin aiki nan take yayin da ya ba da umurnin tuhumar wasu don tabbatar da zargin da ake musu kan badakala a filin jirgin da aka ba da rahoto kwanan nan kana a san matakin da za a dauka akan su.

Kwanturolan Janar, na amfani da wannan damar don tabbatar wa ‘yan kasa da cewa, Hukumar NIS ba za ta lamunta duk wani hali ko nau’i na halin rashin gaskiya ba ga duk Jami’anta, don haka, yana kira ga jama’a da su ci gaba da bada rahoton duk wani nau’in hali na cin zarafi ko rashin gaskiya a bakin aiki da aka ga jami’in hukumar na aikatawa.

NIS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Biyu A Harin Nakiya A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.