• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice (NIS) reshen Jihar Bayelsa za ta fara bayar da sabon ingantaccen fasfo, a wani yunƙuri da hukumar ke yi na sauyawa daga tsohon yayi na fasfon zuwa sabon da aka samar.

Shi dai sabon fasfon yana ƙumshe da abubuwa na tsaro sama da 25, kana an tsara shi a bisa ingancin da duniya ta amince da shi wanda sannu a hankali zai maye gurbin tsohon samfurin fasfon da ake bayarwa.

  • Yadda Aka Ƙaddamar Da Ƙungiyar SURE 4U Domin Jin Ƙan Marasa Galihu

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Bayelsa, ta shawarci masu neman fasfo a yankin jihar su bi ƙa’idar da hukumar ta sa wajen gabatar da buƙatarsu ta hanyar amfani da sadarwar intanet a dukkan matakan da ake bi tun daga cike takardar nema zuwa biyan kuɗi da ɗaukar hoto da sanin ranar karɓa wanda hakan zai hana mai nema faɗawa hannun bara-gurbi masu tatsar kuɗi.

Ita dai NIS ta duƙufa wajen ganin mutane suna samun fasfo ba tare da katsalandan daga wani ba. Ministan Cikin Gida Rauf Aregbesola tare da Kwanturola Janar na NIS Isah Jere Idris za su ƙaddamar da babbar cibiyar fasfon a Jihar Ribas wadda za ta karaɗe ofisoshin fasfo na Jihohin Akwa-Ibom, Bayelsa, da Kuros Ribas.

Sabon ingantaccen fasfon dai yana da tsare-tsare na musamman da aka kasafta zuwa matakai guda uku. Akwai mai shafi 32 da yake aiki na tsawon shekara 5, sai mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 5 da kuma mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 10.
Hanya mafi sauƙi da mutum zai bi ya nemi fasfon ita ce ya shiga adireshin intanet na: passport.immigration.gov.ng, yana shiga zai ga fom sai ya cike tare da biyan kuɗi, duka dai ta intanet. Daga nan sai ya sauke takardar shaidar biyan kuɗi da ta lokacin da aka ba shi na zuwa ɗaukar hoto tare da wallafawa.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Mutum zai ziyarci ofishin fasfo ne kawai a ranar da aka ce ya je, sai ya tafi da abubuwan da aka ce ya tanada ciki har da takardar shaidar biyan kuɗinsa.

 

Wajibi ne dai ga kowane mai neman fasfo ya yi amfani da lambarsa ta shaidar ɗan ƙasa wajen neman fasfo. Wa’adin samun fasfo ga sabbin shiga shi ne mako shida, yayin da na waɗanda za su sabunta kuma bai wuce mako uku ba.

  • https://m.facebook.com/LeadershipNGA/photos/a.251250111575686/4899099793457338/

Domin ƙarin bayani ana iya kiran wannan lambar: 08021819988 ko a ziyarci adireshin NIS na intanet ta: www.immigration.gov.ng


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufar Rungumar Makomar Dan Adam Ta Bai Daya Ta Nuna Inda Duniyarmu Za Ta Dosa

Next Post

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Related

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

3 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

5 hours ago
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami
Labarai

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

6 hours ago
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

7 hours ago
Next Post
Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.