• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice (NIS) reshen Jihar Bayelsa za ta fara bayar da sabon ingantaccen fasfo, a wani yunƙuri da hukumar ke yi na sauyawa daga tsohon yayi na fasfon zuwa sabon da aka samar.

Shi dai sabon fasfon yana ƙumshe da abubuwa na tsaro sama da 25, kana an tsara shi a bisa ingancin da duniya ta amince da shi wanda sannu a hankali zai maye gurbin tsohon samfurin fasfon da ake bayarwa.

  • Yadda Aka Ƙaddamar Da Ƙungiyar SURE 4U Domin Jin Ƙan Marasa Galihu

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Bayelsa, ta shawarci masu neman fasfo a yankin jihar su bi ƙa’idar da hukumar ta sa wajen gabatar da buƙatarsu ta hanyar amfani da sadarwar intanet a dukkan matakan da ake bi tun daga cike takardar nema zuwa biyan kuɗi da ɗaukar hoto da sanin ranar karɓa wanda hakan zai hana mai nema faɗawa hannun bara-gurbi masu tatsar kuɗi.

Ita dai NIS ta duƙufa wajen ganin mutane suna samun fasfo ba tare da katsalandan daga wani ba. Ministan Cikin Gida Rauf Aregbesola tare da Kwanturola Janar na NIS Isah Jere Idris za su ƙaddamar da babbar cibiyar fasfon a Jihar Ribas wadda za ta karaɗe ofisoshin fasfo na Jihohin Akwa-Ibom, Bayelsa, da Kuros Ribas.

Sabon ingantaccen fasfon dai yana da tsare-tsare na musamman da aka kasafta zuwa matakai guda uku. Akwai mai shafi 32 da yake aiki na tsawon shekara 5, sai mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 5 da kuma mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 10.
Hanya mafi sauƙi da mutum zai bi ya nemi fasfon ita ce ya shiga adireshin intanet na: passport.immigration.gov.ng, yana shiga zai ga fom sai ya cike tare da biyan kuɗi, duka dai ta intanet. Daga nan sai ya sauke takardar shaidar biyan kuɗi da ta lokacin da aka ba shi na zuwa ɗaukar hoto tare da wallafawa.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Mutum zai ziyarci ofishin fasfo ne kawai a ranar da aka ce ya je, sai ya tafi da abubuwan da aka ce ya tanada ciki har da takardar shaidar biyan kuɗinsa.

 

Wajibi ne dai ga kowane mai neman fasfo ya yi amfani da lambarsa ta shaidar ɗan ƙasa wajen neman fasfo. Wa’adin samun fasfo ga sabbin shiga shi ne mako shida, yayin da na waɗanda za su sabunta kuma bai wuce mako uku ba.

  • https://m.facebook.com/LeadershipNGA/photos/a.251250111575686/4899099793457338/

Domin ƙarin bayani ana iya kiran wannan lambar: 08021819988 ko a ziyarci adireshin NIS na intanet ta: www.immigration.gov.ng


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufar Rungumar Makomar Dan Adam Ta Bai Daya Ta Nuna Inda Duniyarmu Za Ta Dosa

Next Post

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Related

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

25 minutes ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

5 hours ago
NIS
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

6 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

9 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

12 hours ago
Next Post
Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
NIS

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.