• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice (NIS) reshen Jihar Bayelsa za ta fara bayar da sabon ingantaccen fasfo, a wani yunƙuri da hukumar ke yi na sauyawa daga tsohon yayi na fasfon zuwa sabon da aka samar.

Shi dai sabon fasfon yana ƙumshe da abubuwa na tsaro sama da 25, kana an tsara shi a bisa ingancin da duniya ta amince da shi wanda sannu a hankali zai maye gurbin tsohon samfurin fasfon da ake bayarwa.

  • Yadda Aka Ƙaddamar Da Ƙungiyar SURE 4U Domin Jin Ƙan Marasa Galihu

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Bayelsa, ta shawarci masu neman fasfo a yankin jihar su bi ƙa’idar da hukumar ta sa wajen gabatar da buƙatarsu ta hanyar amfani da sadarwar intanet a dukkan matakan da ake bi tun daga cike takardar nema zuwa biyan kuɗi da ɗaukar hoto da sanin ranar karɓa wanda hakan zai hana mai nema faɗawa hannun bara-gurbi masu tatsar kuɗi.

Ita dai NIS ta duƙufa wajen ganin mutane suna samun fasfo ba tare da katsalandan daga wani ba. Ministan Cikin Gida Rauf Aregbesola tare da Kwanturola Janar na NIS Isah Jere Idris za su ƙaddamar da babbar cibiyar fasfon a Jihar Ribas wadda za ta karaɗe ofisoshin fasfo na Jihohin Akwa-Ibom, Bayelsa, da Kuros Ribas.

Sabon ingantaccen fasfon dai yana da tsare-tsare na musamman da aka kasafta zuwa matakai guda uku. Akwai mai shafi 32 da yake aiki na tsawon shekara 5, sai mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 5 da kuma mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 10.
Hanya mafi sauƙi da mutum zai bi ya nemi fasfon ita ce ya shiga adireshin intanet na: passport.immigration.gov.ng, yana shiga zai ga fom sai ya cike tare da biyan kuɗi, duka dai ta intanet. Daga nan sai ya sauke takardar shaidar biyan kuɗi da ta lokacin da aka ba shi na zuwa ɗaukar hoto tare da wallafawa.

Labarai Masu Nasaba

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Mutum zai ziyarci ofishin fasfo ne kawai a ranar da aka ce ya je, sai ya tafi da abubuwan da aka ce ya tanada ciki har da takardar shaidar biyan kuɗinsa.

 

Wajibi ne dai ga kowane mai neman fasfo ya yi amfani da lambarsa ta shaidar ɗan ƙasa wajen neman fasfo. Wa’adin samun fasfo ga sabbin shiga shi ne mako shida, yayin da na waɗanda za su sabunta kuma bai wuce mako uku ba.

  • https://m.facebook.com/LeadershipNGA/photos/a.251250111575686/4899099793457338/

Domin ƙarin bayani ana iya kiran wannan lambar: 08021819988 ko a ziyarci adireshin NIS na intanet ta: www.immigration.gov.ng


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufar Rungumar Makomar Dan Adam Ta Bai Daya Ta Nuna Inda Duniyarmu Za Ta Dosa

Next Post

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Related

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

2 hours ago
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno
Labarai

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

3 hours ago
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno
Labarai

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

5 hours ago
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu
Labarai

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

7 hours ago
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum
Labarai

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

8 hours ago
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
Labarai

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

8 hours ago
Next Post
Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.