ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

by El-Zaharadeen Umar and Sulaiman
8 months ago
masari

Shugaban kwamitin gudanarwa na hukumar tallafa wa manyan makarantun gaba Sakandire TETFUND, kuma tsohon gwamnan jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello ya jagoranci wani taro na masu ruwa da tsaki akan sha’anin harkokin ilimin a Nijeriya.

Taron dai na da nufin gayyato masana da masu ruwa da tsaki akan sha’anin manyan makarantun gaba sakandire domin su fahimci ayyukan hukumar Sannan su bada gudunmawa da shawara ta yadda za a kara inganta ayyukan hukumar

An gudanar da taron a karo na farko inda masana da kungiyoyin farar hula da ‘yan jaridu da kungiyoyin Malaman jami’o’i da jami’an gwamnati da ‘yan majalisa suka halarta, wanda kuma ya gudanar A Class and Ebent Center, Ibrahim Ibrahim Way, Wuse II, Abuja

ADVERTISEMENT

Bayan kammala taron wakilanmu El-Zaharadeen Umar ya tattauna da shugaban hukumar gudanarwa na asusun tallafawa manyan makarantun gaba da Sakandire TETFUND tsohon gwamnan Jihar Katsina Alhaji Aminu Bello Masari domin Dalili shirya irin wannan taro da kuma manufar da ake san cimmawa.

Ga yadda tattaunawar ta kasance.

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

Dalilin Da Ya Sa PDP Ke Cikin Rikici, Za Ta Dawo Da Karfin Ta —Saraki

 

Shin menene makasudin shirya irin wannan taro na masu ruwa da tsaki akan sha’anin ilimi da aka gudanar a yau?

Makasudin wannan taro shi ne a fadakar da mutane ayyukan wannan hukuma ta TETFUND da take yi, sannan kuma a yi magana da wadanda suka fi amfana da shi wannan tsari na TETFUND. Kamar jami’ai da makarantu da kuma dalibai sannan kuma a karbi shawarwari ga jama’a akan yadda za a bunkasa wannan aikin na hukumar tallafawa manyan makarantu na gaba da Sakandire a Nijeriya.

Wannan shi ne makasudi kuma na farko da ake san a jawo al’umma a ciki su dan abinda ake yi da yadda ake kashe kudaden da kuma yadda ake tarawa da makasudin tara su da makarantun da ake ba kudaden da kuma su makarantu yadda suke amfani da kudin

 

Shin kamar bangarori nawa ne suka halarci wannan taro na masu ruwa da tsaki a wannan hukuma ta asusun TETFUND?

Aminu Bello Masari: Na farko akwai bangarorin makarantu da Dalibai da ‘yan jarida da masu bukata ta musamman da kungiyoyin Malaman jami’o’i wata ASUU da da COUSU da duk masu ruwa da tsaki akan harkar ilmin gaba da Sakandire da kungiyoyin farar hula duk sun halarci wannan taro, bayan jami’an gwamnati wadanda suka zo daga fanni-fanni da tsofaffin shugabanni da majalisar tarayya da suke da hakkin kudaden da ake kashewa baki daya.

 

Jama’a da dama sun yi magana akan zama wasu sun mika kokon barar su akan ilmin gaba da Sakandire wani mataki zaku dauka a kan haka?

Daman ma’anar wancan zama shi ne domin a samu karin shawarwari daga al’umma da masana ta yadda za a cigaba da lissafin kasafin kudi na shekarar 2026, samun wadannan shawarwari za mu zauna mu kalle su, mu duba wadanda za su iya yiyuwa bana, wasu kuma sai an tura gaba, amma dai za a yi wani abu akan shawarwarin da aka samu insha’Allahu.

 

Masu bukata ta musamman sun samu wakilci kuma har sun mika bukatun su, me zaka ce game da haka?

To, na farko dai su masu bukata ta musamman darkatan da ke kula da gine-gine ya ce to yanzu dole ne duk ginin da za a yi dai an tabbatar da yana da tsari na kula da masu bukata ta musamman. Kuma sun kawo bukatar suna san a yi masu wani gurbi a ofishin shi sakatare na hukumar tallafawa manyan makarantun gaba da Sakandire, wannan kuma wani abu ne da sai mun zauna wajen taro zamu kalli abubuwan sannan abinda ke yiyuwa kuma shi za a yi.

 

A takaice me kake son cimmawa na ganin an ciyar da wannan hukuma ta TETFUND gaba?

Ai babban al’amari shi ne, a sanya mutane a cikin hidimar su san abinda ake yi, kuma su ba da shawarwari yadda za a kara bunkasa abin da ita wannan ma’aikata take yi, kudi ake amsa masu yawa kuma wajibi ne a gayawa jama’a yadda ake sarrafa wadannan kudaden a dukkan jami’o’in gwamnatin tarayya kusan 250 banda kwalejojin da sauran su ba wanda bai amfana da wadannan kudadai duk shekara.

 

Zuwa yanzu an kashe nawa a wannan hukuma mai tallafa wa manyan makarantun gaba da Sakandire a Nijeriya?

Yanzu abin da za mu iya cewa shi ne mun yi kasafin kudi, wanda zuwa yanzu an baiwa su makarantun daunin su na kaso hamsin (%50) bisa dari wanda yanzu lissafin da aka yi ya wuce biliyan 500 wanda aka ba su Makarantun a hannun su, to kuma za su kawo yadda za su kashe kudaden, sannan sauran an yi aikin lafiya da su wanda yanzu haka an fada a wajen taron da kuma aikin wuta da aikin tsaro duk wadannan wurare ne da aka sanya kudi da ayyuka na musamman.

masari
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
masari
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu
Tattaunawa

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

April 10, 2026
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Tattaunawa

Dalilin Da Ya Sa PDP Ke Cikin Rikici, Za Ta Dawo Da Karfin Ta —Saraki

April 4, 2026
Zan Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Bunkasa Yanki Na —Sarkin Tilden Fulani
Tattaunawa

Zan Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Bunkasa Yanki Na —Sarkin Tilden Fulani

March 28, 2026
Next Post
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.