• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Ilmantar Da Kamfanoni Kan Ƙa’idojin Aiki Da ‘Yan Ƙasashen Waje

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
NIS Reshen Jihar Ribas Ta Ilmantar Da Kamfanoni Kan Ƙa’idojin Aiki Da ‘Yan Ƙasashen Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), reshen Jihar Ribas ta gudanar da wani taron ƙara wa juna sani domin wayar da kai a kan ayyukan ‘yan ƙasashen waje a kamfanoni da kuma hulɗoɗin zuba jari a Birnin Fatakwal, babban birnin jihar.

Kwanturolan hukumar ta NIS na Jihar Ribas wanda har ila yau shi ne babban mai ilmantarwa a taron, CIS Sunday James, ya nemi kamfanoni da hukumomi kar su yi ƙasa a gwiwa a kan haƙƙoƙin da suka rataya a wuyansu na ɗaukar ‘yan ƙasa aiki waɗanda suka yi ilimi da kuma samun ƙwarewar aiki. A cewarsa, yin hakan ƙa;ida ce da ke cikin tsarin gudanar da ayyukan kamfanoni da aka bai wa lasisin ayyuka da ‘yan ƙasashen waje inda ake buƙatar kamfanonin su ɗauki ‘yan ƙasa da za su koyi aiki tare da maye gurbin ‘yan ƙasashen waje da zarar sun ƙware a fannonin da suke aikin a Nijeriya.

Har ila yau, a yayin gudanar da taron, an tattauna muhimman batutuwa da suka shafi yadda ake keta dokokin shige da fice domin ilmantar da mahalartan daga kamfanoni da hukumomi abubuwan da suka kamata su riƙa gudanarwa tare da tabbatar da cewa suna biyan kuɗin ƙa’ida na ‘yan ƙasashen waje da ke aiki a ƙarƙashinsu duk wata, da irin bizar da ta kamata a riƙa amfani da ita da hanyoyin da suka kamata a bi wurin sallamar ma’aikaci, da yadda za a nemi wasiƙar da za ta wanke mutum daga zargin aikata mugun laifi da ta sa aka kores shi daga aiki kafin ya ajiye aiki ko sallamarsa da sauransu.

NIS

Wakazalika, an shawarci masu ɗaukar aiki su riƙa goge sunayen ‘yan ƙasar waje da suka sallama daga aiki daga cikin jerin waɗanda suke ƙarƙashin kulawarsu bayan sun bi duk matakai da ƙa’ida ta shimfiɗa domin waɗanda aka sallamar su iya samun damar yin aiki a wasu wuraren na daban.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Bugu da ƙari, an ilmantar da kamfanonin a kan bin ƙa’idojin da aka shimfiɗa na sauya wa ‘yan ƙasashen waje sashen da suke aiki ko ɗaukar sabbi ta hanyar amfani da takardu da bizar da suka dace a koyaushe, domin kauce wa fushin doka kamar yadda aka tanadi hukunci a dokar shige da fice ta 2015 da ta 2017 da sauran dokoki na ƙasa da suka shafi hakan.

Kamar yadda Sunday James ya yi ƙarin haske, dokar ɓangaren zartarwa ta yi tanadin sauƙaƙa hada-hadar kasuwanci da ‘yan ƙasashen waje, wajen shigar da ‘yan ƙasa su ci gajiyar abin ta fuskar kimiyya da fasaha da ƙara buɗe hanyoyin samar wa matasan ƙasa ayyukan yi waɗanda suka yi karatu kuma suka samu tantancewar da ta dace daga wurin ƙwararru.

Ƙaramar Mataimakiyar Kwanturola Janar mai kula da Shiyya ta Biyar (Zone E) ta NIS wadda ta ƙunshi Jihohin Abiya, Akwa Ibom, Kuros Riba, Ebonyi, Imo da kuma Ribas wadda ta halarci taron a matsayin babbar baƙuwa, ta shawarci mahalarta taron daga kamfanoni da hukumomi su bi dokokin da aka shimfiɗa na aiki da ‘yan ƙasashen waje sau da ƙafa domin ci gaban ƙasa musamman ta fuskar bayar da bayanan wadanda suke aiki tare da su da kuma tabbatar da cewa suna yin abubuwan da suka dace.

Ɗaukacin mahalarta taron na NIS reshen Jihar Ribas daga kamfanoni da hukumomi sun bayar da gudunmawa a wurin taron ta hanyar neman ƙarin haske kan wasu abubuwa da suka shige musu duhu da kuma neman ƙarin bayani kan wasu kurakurai da ake cin karo da su saboda ajizanci na ɗan’adam wanda jami’an na NIS ke ganowa yayin da ɗan ƙasar waje ya zo shiga ƙasa, tare da jaddada buƙatar hukumar ta shige da fice ta riƙa aiki kafaɗa da kafaɗa da kamfanoni domin tabbatar da komai ya tafi daidai-wdaida yayin shiga ko fita ƙasa.

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiKamfanoniKasashen WajeNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Tsare Tsohon Gwamnan Benuwe, Ortom

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Dokar Ta-Baci Kan Masu Kwacen Waya

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

9 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

12 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

12 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

14 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

14 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

15 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Dokar Ta-Baci Kan Masu Kwacen Waya

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Dokar Ta-Baci Kan Masu Kwacen Waya

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.