ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Ilmantar Da Kamfanoni Kan Ƙa’idojin Aiki Da ‘Yan Ƙasashen Waje

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), reshen Jihar Ribas ta gudanar da wani taron ƙara wa juna sani domin wayar da kai a kan ayyukan ‘yan ƙasashen waje a kamfanoni da kuma hulɗoɗin zuba jari a Birnin Fatakwal, babban birnin jihar.

Kwanturolan hukumar ta NIS na Jihar Ribas wanda har ila yau shi ne babban mai ilmantarwa a taron, CIS Sunday James, ya nemi kamfanoni da hukumomi kar su yi ƙasa a gwiwa a kan haƙƙoƙin da suka rataya a wuyansu na ɗaukar ‘yan ƙasa aiki waɗanda suka yi ilimi da kuma samun ƙwarewar aiki. A cewarsa, yin hakan ƙa;ida ce da ke cikin tsarin gudanar da ayyukan kamfanoni da aka bai wa lasisin ayyuka da ‘yan ƙasashen waje inda ake buƙatar kamfanonin su ɗauki ‘yan ƙasa da za su koyi aiki tare da maye gurbin ‘yan ƙasashen waje da zarar sun ƙware a fannonin da suke aikin a Nijeriya.

Har ila yau, a yayin gudanar da taron, an tattauna muhimman batutuwa da suka shafi yadda ake keta dokokin shige da fice domin ilmantar da mahalartan daga kamfanoni da hukumomi abubuwan da suka kamata su riƙa gudanarwa tare da tabbatar da cewa suna biyan kuɗin ƙa’ida na ‘yan ƙasashen waje da ke aiki a ƙarƙashinsu duk wata, da irin bizar da ta kamata a riƙa amfani da ita da hanyoyin da suka kamata a bi wurin sallamar ma’aikaci, da yadda za a nemi wasiƙar da za ta wanke mutum daga zargin aikata mugun laifi da ta sa aka kores shi daga aiki kafin ya ajiye aiki ko sallamarsa da sauransu.

ADVERTISEMENT

NIS

Wakazalika, an shawarci masu ɗaukar aiki su riƙa goge sunayen ‘yan ƙasar waje da suka sallama daga aiki daga cikin jerin waɗanda suke ƙarƙashin kulawarsu bayan sun bi duk matakai da ƙa’ida ta shimfiɗa domin waɗanda aka sallamar su iya samun damar yin aiki a wasu wuraren na daban.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Bugu da ƙari, an ilmantar da kamfanonin a kan bin ƙa’idojin da aka shimfiɗa na sauya wa ‘yan ƙasashen waje sashen da suke aiki ko ɗaukar sabbi ta hanyar amfani da takardu da bizar da suka dace a koyaushe, domin kauce wa fushin doka kamar yadda aka tanadi hukunci a dokar shige da fice ta 2015 da ta 2017 da sauran dokoki na ƙasa da suka shafi hakan.

Kamar yadda Sunday James ya yi ƙarin haske, dokar ɓangaren zartarwa ta yi tanadin sauƙaƙa hada-hadar kasuwanci da ‘yan ƙasashen waje, wajen shigar da ‘yan ƙasa su ci gajiyar abin ta fuskar kimiyya da fasaha da ƙara buɗe hanyoyin samar wa matasan ƙasa ayyukan yi waɗanda suka yi karatu kuma suka samu tantancewar da ta dace daga wurin ƙwararru.

Ƙaramar Mataimakiyar Kwanturola Janar mai kula da Shiyya ta Biyar (Zone E) ta NIS wadda ta ƙunshi Jihohin Abiya, Akwa Ibom, Kuros Riba, Ebonyi, Imo da kuma Ribas wadda ta halarci taron a matsayin babbar baƙuwa, ta shawarci mahalarta taron daga kamfanoni da hukumomi su bi dokokin da aka shimfiɗa na aiki da ‘yan ƙasashen waje sau da ƙafa domin ci gaban ƙasa musamman ta fuskar bayar da bayanan wadanda suke aiki tare da su da kuma tabbatar da cewa suna yin abubuwan da suka dace.

Ɗaukacin mahalarta taron na NIS reshen Jihar Ribas daga kamfanoni da hukumomi sun bayar da gudunmawa a wurin taron ta hanyar neman ƙarin haske kan wasu abubuwa da suka shige musu duhu da kuma neman ƙarin bayani kan wasu kurakurai da ake cin karo da su saboda ajizanci na ɗan’adam wanda jami’an na NIS ke ganowa yayin da ɗan ƙasar waje ya zo shiga ƙasa, tare da jaddada buƙatar hukumar ta shige da fice ta riƙa aiki kafaɗa da kafaɗa da kamfanoni domin tabbatar da komai ya tafi daidai-wdaida yayin shiga ko fita ƙasa.

 

 

 

NIS
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Dokar Ta-Baci Kan Masu Kwacen Waya

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Dokar Ta-Baci Kan Masu Kwacen Waya

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.