ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Ilmantar Da Kamfanoni Kan Ƙa’idojin Aiki Da ‘Yan Ƙasashen Waje

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), reshen Jihar Ribas ta gudanar da wani taron ƙara wa juna sani domin wayar da kai a kan ayyukan ‘yan ƙasashen waje a kamfanoni da kuma hulɗoɗin zuba jari a Birnin Fatakwal, babban birnin jihar.

Kwanturolan hukumar ta NIS na Jihar Ribas wanda har ila yau shi ne babban mai ilmantarwa a taron, CIS Sunday James, ya nemi kamfanoni da hukumomi kar su yi ƙasa a gwiwa a kan haƙƙoƙin da suka rataya a wuyansu na ɗaukar ‘yan ƙasa aiki waɗanda suka yi ilimi da kuma samun ƙwarewar aiki. A cewarsa, yin hakan ƙa;ida ce da ke cikin tsarin gudanar da ayyukan kamfanoni da aka bai wa lasisin ayyuka da ‘yan ƙasashen waje inda ake buƙatar kamfanonin su ɗauki ‘yan ƙasa da za su koyi aiki tare da maye gurbin ‘yan ƙasashen waje da zarar sun ƙware a fannonin da suke aikin a Nijeriya.

Har ila yau, a yayin gudanar da taron, an tattauna muhimman batutuwa da suka shafi yadda ake keta dokokin shige da fice domin ilmantar da mahalartan daga kamfanoni da hukumomi abubuwan da suka kamata su riƙa gudanarwa tare da tabbatar da cewa suna biyan kuɗin ƙa’ida na ‘yan ƙasashen waje da ke aiki a ƙarƙashinsu duk wata, da irin bizar da ta kamata a riƙa amfani da ita da hanyoyin da suka kamata a bi wurin sallamar ma’aikaci, da yadda za a nemi wasiƙar da za ta wanke mutum daga zargin aikata mugun laifi da ta sa aka kores shi daga aiki kafin ya ajiye aiki ko sallamarsa da sauransu.

ADVERTISEMENT

NIS

Wakazalika, an shawarci masu ɗaukar aiki su riƙa goge sunayen ‘yan ƙasar waje da suka sallama daga aiki daga cikin jerin waɗanda suke ƙarƙashin kulawarsu bayan sun bi duk matakai da ƙa’ida ta shimfiɗa domin waɗanda aka sallamar su iya samun damar yin aiki a wasu wuraren na daban.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Bugu da ƙari, an ilmantar da kamfanonin a kan bin ƙa’idojin da aka shimfiɗa na sauya wa ‘yan ƙasashen waje sashen da suke aiki ko ɗaukar sabbi ta hanyar amfani da takardu da bizar da suka dace a koyaushe, domin kauce wa fushin doka kamar yadda aka tanadi hukunci a dokar shige da fice ta 2015 da ta 2017 da sauran dokoki na ƙasa da suka shafi hakan.

Kamar yadda Sunday James ya yi ƙarin haske, dokar ɓangaren zartarwa ta yi tanadin sauƙaƙa hada-hadar kasuwanci da ‘yan ƙasashen waje, wajen shigar da ‘yan ƙasa su ci gajiyar abin ta fuskar kimiyya da fasaha da ƙara buɗe hanyoyin samar wa matasan ƙasa ayyukan yi waɗanda suka yi karatu kuma suka samu tantancewar da ta dace daga wurin ƙwararru.

Ƙaramar Mataimakiyar Kwanturola Janar mai kula da Shiyya ta Biyar (Zone E) ta NIS wadda ta ƙunshi Jihohin Abiya, Akwa Ibom, Kuros Riba, Ebonyi, Imo da kuma Ribas wadda ta halarci taron a matsayin babbar baƙuwa, ta shawarci mahalarta taron daga kamfanoni da hukumomi su bi dokokin da aka shimfiɗa na aiki da ‘yan ƙasashen waje sau da ƙafa domin ci gaban ƙasa musamman ta fuskar bayar da bayanan wadanda suke aiki tare da su da kuma tabbatar da cewa suna yin abubuwan da suka dace.

Ɗaukacin mahalarta taron na NIS reshen Jihar Ribas daga kamfanoni da hukumomi sun bayar da gudunmawa a wurin taron ta hanyar neman ƙarin haske kan wasu abubuwa da suka shige musu duhu da kuma neman ƙarin bayani kan wasu kurakurai da ake cin karo da su saboda ajizanci na ɗan’adam wanda jami’an na NIS ke ganowa yayin da ɗan ƙasar waje ya zo shiga ƙasa, tare da jaddada buƙatar hukumar ta shige da fice ta riƙa aiki kafaɗa da kafaɗa da kamfanoni domin tabbatar da komai ya tafi daidai-wdaida yayin shiga ko fita ƙasa.

 

 

 

NIS
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Dokar Ta-Baci Kan Masu Kwacen Waya

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Dokar Ta-Baci Kan Masu Kwacen Waya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.